• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 16 ga watan nan da muke ciki, rana ce ta tabbatar da wadatar abinci a duniya. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da wannan batu, da ya zama abin da gwamnatocin kasa da kasa suke mai da hankali kansa a ko da yaushe? Bari mu tantance kokarin da Sin ta yi a wannan bangare, da gudunmawar da take bayarwa duniya.

 

A shekarar 1949, lokacin da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin, yawan hatsin da Sin ta samu shekara daya bai wuce ton miliyan 113.2 ba. Amma a shekarar 2023, wannan adadin ya kai ton miliyan 695, kuma an tabbatar da samun yawan hatsin da ya kai kimanin ton miliyan 650 a cikin shekaru 9 a jere, lamarin da ya sanya Sin samun yabanya mai yalwa cikin shekaru 20 a jere. Kana matsakacin yawan hatsin da kowane Basine ya samu a duk shekara ya kai kilo 493, adadin da ya zarce kilo 400, wanda ya zama ma’aunin duniya na samun wadatar abinci ga ko wane mutum. Abun da ya bayyana cewa, Sinawa na samun wadatar abinci bisa jagorantar da gwamnatinsu ta yi, gami da kokarinsu.

  • Yawan Karuwar GDPn Sin Daga Watan Janairu Zuwa Satumban Bana Ya Kai 4.8% Bisa Na Makamancin Lokacin A Bara
  • Li Qiang Ya Halarci Taron Majalisar Shugabannin Gwamnatocin Kasashe Mambobin SCO Karo Na 23

Mene ne dalilin da ya sa aka samu wannan nasara? Shi ne domin tsarin kare gonaki na kasar, da yadda take yayata fasahar aikin gona. Ya zuwa karshen shekarar 2023, yawan ingantattun gonakin da Sin ta mallaka ya kai fiye da muraba’in kilomita dubu 667. Kuma ba tabbatar da yawansu kadai kasar Sin take yi ba, tana dukufa kan tabbatar da ingancinsu. Kazalika, yawan gudunmawa ta fuskar kimiyya da fasaha da aka samar a bangaren aikin gona a shekarar 2023 ya kai kashi 63.2%, adadin da ya karu da kashi 8.7% bisa na shekarar 2012, matakin da ya sa Sin zama daya daga cikin kasashe mafiya karfin kimiyya da fasahar aikin gona. Sabbin nau’o’in kimiyya da fasaha da Sin take bayarwa, na taimakon kokarin tabbatar da wadatar abinci.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Ban da wannan kuma, hanyar da Sin take bi na tabbatar da wadatar abinci, ya zama abun koyi ga kasashe daban daban, kuma Sin tana hadin gwiwa da sauran kasashe wajen yada fasahohinta. Alali misali, kasar Madagascar, ta rungumi fasahar noman shinkafar da aka tagwaita ta Sin, inda yawan shinkafar da ake nomanta a Madagascar ya kai kadada dubu 70, kana yawan hatsin da ake girba kan kadada daya ya kai ton 7, wani lokaci har ya kan kai ton 12, adadin da ya ninka har sau 2 bisa na nau’in shinkafar asali da ake nomansu a kasar. Ta la’akari da bukatun da ke akwai a kasar Madagascar a duk shekara, za a samu damar tabbatar da wadatar abinci a kasar, idan aka kara shuka irin shinkafar Sin a gonaki masu fadin kadada dubu 100. Domin tunawa da taimakon da Sin ta ba kasar a bangaren shuka shinkafar da aka tagwaita, Madagascar ta buga hoton shinkafar Sin a kan takardar kudinta.

 

Sin ta taka rawar gani wajen tabbatar da wadatar abinci. Kuma tana kokarin gabatar da dabarunta ga sauran kasashe. Shi ya sa, karin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afrika, ke da damar tabbatar da wadatar abinci, ta hanyar amfani da fasahar Sin. Sinawa su kan ce “More tare da sauran mutane ya fi jin dadin wani abu mutum daya kadai ”. Sin na son raba dabararta ta hanyar hadin gwiwa da sauran kasashe a dukkan fannoni. (MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Ne Ke Tallafa Wa Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Da Kudade?

Next Post

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Related

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

2 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

2 hours ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

18 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

20 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

21 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

23 hours ago
Next Post
Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.