ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Ranar 16 ga watan nan da muke ciki, rana ce ta tabbatar da wadatar abinci a duniya. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da wannan batu, da ya zama abin da gwamnatocin kasa da kasa suke mai da hankali kansa a ko da yaushe? Bari mu tantance kokarin da Sin ta yi a wannan bangare, da gudunmawar da take bayarwa duniya.

 

A shekarar 1949, lokacin da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin, yawan hatsin da Sin ta samu shekara daya bai wuce ton miliyan 113.2 ba. Amma a shekarar 2023, wannan adadin ya kai ton miliyan 695, kuma an tabbatar da samun yawan hatsin da ya kai kimanin ton miliyan 650 a cikin shekaru 9 a jere, lamarin da ya sanya Sin samun yabanya mai yalwa cikin shekaru 20 a jere. Kana matsakacin yawan hatsin da kowane Basine ya samu a duk shekara ya kai kilo 493, adadin da ya zarce kilo 400, wanda ya zama ma’aunin duniya na samun wadatar abinci ga ko wane mutum. Abun da ya bayyana cewa, Sinawa na samun wadatar abinci bisa jagorantar da gwamnatinsu ta yi, gami da kokarinsu.

ADVERTISEMENT
  • Yawan Karuwar GDPn Sin Daga Watan Janairu Zuwa Satumban Bana Ya Kai 4.8% Bisa Na Makamancin Lokacin A Bara
  • Li Qiang Ya Halarci Taron Majalisar Shugabannin Gwamnatocin Kasashe Mambobin SCO Karo Na 23

Mene ne dalilin da ya sa aka samu wannan nasara? Shi ne domin tsarin kare gonaki na kasar, da yadda take yayata fasahar aikin gona. Ya zuwa karshen shekarar 2023, yawan ingantattun gonakin da Sin ta mallaka ya kai fiye da muraba’in kilomita dubu 667. Kuma ba tabbatar da yawansu kadai kasar Sin take yi ba, tana dukufa kan tabbatar da ingancinsu. Kazalika, yawan gudunmawa ta fuskar kimiyya da fasaha da aka samar a bangaren aikin gona a shekarar 2023 ya kai kashi 63.2%, adadin da ya karu da kashi 8.7% bisa na shekarar 2012, matakin da ya sa Sin zama daya daga cikin kasashe mafiya karfin kimiyya da fasahar aikin gona. Sabbin nau’o’in kimiyya da fasaha da Sin take bayarwa, na taimakon kokarin tabbatar da wadatar abinci.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Ban da wannan kuma, hanyar da Sin take bi na tabbatar da wadatar abinci, ya zama abun koyi ga kasashe daban daban, kuma Sin tana hadin gwiwa da sauran kasashe wajen yada fasahohinta. Alali misali, kasar Madagascar, ta rungumi fasahar noman shinkafar da aka tagwaita ta Sin, inda yawan shinkafar da ake nomanta a Madagascar ya kai kadada dubu 70, kana yawan hatsin da ake girba kan kadada daya ya kai ton 7, wani lokaci har ya kan kai ton 12, adadin da ya ninka har sau 2 bisa na nau’in shinkafar asali da ake nomansu a kasar. Ta la’akari da bukatun da ke akwai a kasar Madagascar a duk shekara, za a samu damar tabbatar da wadatar abinci a kasar, idan aka kara shuka irin shinkafar Sin a gonaki masu fadin kadada dubu 100. Domin tunawa da taimakon da Sin ta ba kasar a bangaren shuka shinkafar da aka tagwaita, Madagascar ta buga hoton shinkafar Sin a kan takardar kudinta.

 

Sin ta taka rawar gani wajen tabbatar da wadatar abinci. Kuma tana kokarin gabatar da dabarunta ga sauran kasashe. Shi ya sa, karin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afrika, ke da damar tabbatar da wadatar abinci, ta hanyar amfani da fasahar Sin. Sinawa su kan ce “More tare da sauran mutane ya fi jin dadin wani abu mutum daya kadai ”. Sin na son raba dabararta ta hanyar hadin gwiwa da sauran kasashe a dukkan fannoni. (MINA)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.