ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

by Bello Hamza
2 years ago
Buratai

Gidauniyar TY Burutai ta mika sakon taya murna ga Kwamanda Tunde Giwa Daramola kan zama shugaban kungiyar masu tseren kwale kwale ta Jihar Ondo.

Wanda Gwamnan jihar wato Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya nada shi. Sakon taya murnar ta fito ne ta hannun Shugaban Gidauniyar, Ibrahim Dahiru Danfulani Sadaukin Gwarkuwan Keffi/Betara Biu wanda ya mika wa manema labarai.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Xi Ya Amsa Wasikar Wakilan Daliban Da Suka Halarci Gasar Kere-Keren Kimiyya Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin

Kwamanda Tunde Giwa Daramola mai ritaya mutum ne da ya yi fice daga cikin tsarraraki kuma babban abin alfahrin dalban makarantar sojoji da ke Kaduna aji na 29. Ba kawai babban soja ba ne ya kuma kasance kwararren ma’aikaci. Yanayin tafiyar da al’amuran shi da kuma maida hankali wajen aiki da kuma wasannin motsa jiki ya zamar dashi wanda ya cancanci wannan mukami.

ADVERTISEMENT

Uban Gidauniyar TY Burutai, wato Ambasada Janar Tukur Yusuf Buratai tsowan shugaban sojojin Nijeriya ya yi matukar murna da jin dadi game da wannan nadin da a ka yi ma Kwamanda Giwa Daramola.

Ya Kuma jadadda muhimmancin samun shugaba kamar Giwa Daramola a shugabancin wannan kungiya. A cewar sa; “Kwamanda Giwa Daramola yana da ruhin dagiya da kwarewa a harkar motsa jiki wanda matasan mu suke bukata a matsayin abin koyi” Ya kara da cewa “Kwarewar shi da kuma maida hankalin shi ga ci gaba ba bu shakka zai daga Kungiyar zuwa matakin da ya kamata”

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Gidauniyar tana alfahari da tallafa wa shugabanni kaman Kwamanda Giwa Daramola wanda suka tsayu da gaskiya da rikon amana a wajen aiki. Muna da yakini karkashin jagorancinshi na Shugaban kungiyar Masu Tseren Kwale kwale Na Jihar Ondo zai samar da ci gaba da sabbin masu wasannin motsa jiki a fadin jihar.

Muna jinjina wa gwamnatin jihar Ondo a kan wannan nadi inda gwamnan yayi duba da kwarewa a harkar tsaro da kuma kokari a fannin motsa jiki wajen wannan nadin. Gidauniyar TY Buratai ta shirya tsaf domin ganin irin ci gaban da za a samu karkashin shugabancin Kwamanda Giwa Daramola a jihar baki daya.

A halin yanzu yabo da jinjina sai kara fitowa yake yi ga shugaban kasa Tinubu a kan yadda ya dauki sashen samar da wutar lantarki a Nijeriya da matukar muhimmanci. Yabo na baya-bayan nan ya fito daga wata kallabi a tsakanin rawunna, Injiniya Amina Ahmed a yayin babban taron makashi na kasa da aka yi a garin Legas a makon jiya.

Taron ya tara masana daga sasan kasar inda aka tatauna yadda za a bunkaasa hanyoyin samar da makashi ga al’ummar Nijeriya gaba daya

Ta bayyana cewa, samar da cikakken wutar lantarki zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin al’umma. Ta ce, bunkasa hanyoyin samar da lantarki ta hanyar hasken rana, zai taimaka wajen bunkasa sana’o’in al’ummar karkara.

Daga nan kuma Injiniya Amina Ahmed ta yi kira gan mata musamman na karkara da su nemi Ilimi tare da rike sana’a, “Ba sai sun nemi sana’a ko aikin gwamnati ba, domin a wannan zamanin, gwamnmati ba za ta iya samar wa da al’umma aiki gaba daya ba, a kan haka ta nemi sauran al’umma musamman masu hannu da shuni da su rika tallafa wa matasan da ke unguwanni ko garuruwansu da shawarwari da kuma tallafi don su samu dogaro da kawunansu.

Daga karshe ta yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a kan yadda ya dauki lamarin samar da wutar lantarki da matukar muhimanci. Za a iya lura da haka ne ta hanyar da ya zabi wadanda suke jagorantar ma’aikatar wutar lantarki musamman Minista Hon Adebayo Adelabu, ‘Hon Adebayo Adelabu ya jajirce wajen tattabar da an tsaftace harkar bayar da wutar lantarki a Nijeriya, in ji ta.

Buratai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC - Kwamishinan Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.