• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ta Yi Nasarar Saukaka Fatara Da Raya Karkara A Gomman Shekaru

by CMG Hausa
3 years ago

Sanin kowa ne cewa Sin kasa ce wacce ta dauki yaki da fatara da muhimmanci, musanmman ma a yankunan karkara inda masu fama da kangin talauci suka fi yawa. Sin dai kasa ce mai tasowa da ta fi kowace girma a duniya kuma tana gaba-gaba a kan yaki da fatara ko kuma talauci a yayin da ta dauki matakai wadanda suka sa ta kawar da kangin talauci daga dukkan fannoni zuwa shekarar 2020.

Wannan cimma nasara dai yana da inganci mai yawa a rayuwar jama’a, da tattalin arziki, da yanayin tsarin gudanar da mulki.

Matakan dai da aka fi ba da muhimmanci a yaki da fatara da raya karkara su ne kamar: fifita harkar noma a kasafin kudi na kasa, da tallafi ga manoma da masu fama da fatara, da bayar da bashi maras yawan riba, da cire haraji a kan manoma da kayan amfanin gona, da bada tallafi a kan kayan aikin gona da kuma saukaka biyan kudi daga ’yan makaranta na karkara. Ana kuma shawartar manoma da su rika shiga kungiyoyin hadin gwiwa domin samun ci gaba da kuma bunkasa jarinsu.

A cikin hanyoyin da tsarin ya kunsa dai sun hada da zuba jari da bunkasa ababen more rayuwa da bunkasa fannin noma da bada tallafi, da bada basusssuka marasa kudin ruwa, haka kuma gwamnati na fadakar da manyan kamfanoni da su zuba jari su hada kai da kananan ’yan kasuwa musamman wadanda ke karkara. Lallai abin jinjinawa ne yadda wannan shiri ya yi nasara a kan saukaka fatara da kuma raya karkara a cikin shekaru goman da suka wuce.

A shekarun baya dai lokacin da na samu damar kai ziyara kasar Sin a yayin da na je wasu larduna wadanda suka hada da Beijing, da Shanghai, da Anhui, da Jiangsu, da Fujian, da Shaanxi.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Abubuwan da suka fi burge ni a shirin yaki da fatara na kasar Sin a nan shi ne kokarin da samari da suka kammala karatun jami’o’i suke yi a kan wani shiri wanda aka dauka su domin aiki da taimakawa a kauyuka don ganin iyalai masu fatara su samu kudaden shiga ta hanyoyi da dama musamman noma, da kiwon dabbobi, da sana’o’i domin fitar da su daga kuncin fatara.

Wani abun burgewar kuma da na lura da shi a cikin ziyarce-ziyarce na a cikin kasar shi ne wato, manoma ba su biyan kudi a manyan hanyoyi wato “toll gate” in dai har sun dauko kayan amfanin gona. Suna wucwe ne kyauta, kuma wannan duk yana cikin tsarin tallafi da rage fatara ne.
Bugu da kari, a sakamakon wannan nauyi da jam’iyyar Kwaminis ta kasar ta dauka, an samu cimma nasarar saukaka fatara da kuma bunkasa yankunan karkara a gomman shekarun da suka gabata a karkashin shirin, wanda aka ayyana a taro na kasa na 18 na jam’iyyar Kwaminis ta kasar a shekarar 2012.

A wannan lokaci ne aka kaddamar da shirin kuma aka tashi gaba daya domin cimma nasarar kakkabe fatara wanda a karshe aka yi nasarar fitar da mutanen da talaucin ya yi ma katutu fiye da miliyan 100. A nan dai ina iya cewa samar da abinci ta fannin fadada harkar noma da raya karkara ne babbar nasara domin a yau, kasar Sin tana ci da kanta duk da tana da yawan mutanen da ya kai biliyan 1.4, dan haka kuma ana samun karin ci gaba a kauyuka.

A sakamakon nasarar da kasar Sin ta samu na cimma burinta na kawar da talauci da raya karkara, kasashen Afirka ma za su iya koyi da matakan da kasar Sin ta dauka domin saukaka fatara a kasashensu.

A Najeriya, a misali, gwamnati ta dauki irin wannan darasi a yayin da ta bullo da shirin bunkasa noman shinkafa ta hanyar bayar da basussuka masu karamar riba da tallafi ga manoma ta hanyar samar da kayan aikin gona da takin zamani. Ta wannan darasi, manoma da dama sun samu ci gaba kuma kasar Najeriya ta samu bunkasar tattalin arziki da kuma rage kudin fita da ake amfani da su wajen shigowa da shinkafar a shekarun baya. (Mai sharhi: Lawal Sale)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.