• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ta Yi Nasarar Saukaka Fatara Da Raya Karkara A Gomman Shekaru

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ta Yi Nasarar Saukaka Fatara Da Raya Karkara A Gomman Shekaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa Sin kasa ce wacce ta dauki yaki da fatara da muhimmanci, musanmman ma a yankunan karkara inda masu fama da kangin talauci suka fi yawa. Sin dai kasa ce mai tasowa da ta fi kowace girma a duniya kuma tana gaba-gaba a kan yaki da fatara ko kuma talauci a yayin da ta dauki matakai wadanda suka sa ta kawar da kangin talauci daga dukkan fannoni zuwa shekarar 2020.

Wannan cimma nasara dai yana da inganci mai yawa a rayuwar jama’a, da tattalin arziki, da yanayin tsarin gudanar da mulki.

Matakan dai da aka fi ba da muhimmanci a yaki da fatara da raya karkara su ne kamar: fifita harkar noma a kasafin kudi na kasa, da tallafi ga manoma da masu fama da fatara, da bayar da bashi maras yawan riba, da cire haraji a kan manoma da kayan amfanin gona, da bada tallafi a kan kayan aikin gona da kuma saukaka biyan kudi daga ’yan makaranta na karkara. Ana kuma shawartar manoma da su rika shiga kungiyoyin hadin gwiwa domin samun ci gaba da kuma bunkasa jarinsu.

A cikin hanyoyin da tsarin ya kunsa dai sun hada da zuba jari da bunkasa ababen more rayuwa da bunkasa fannin noma da bada tallafi, da bada basusssuka marasa kudin ruwa, haka kuma gwamnati na fadakar da manyan kamfanoni da su zuba jari su hada kai da kananan ’yan kasuwa musamman wadanda ke karkara. Lallai abin jinjinawa ne yadda wannan shiri ya yi nasara a kan saukaka fatara da kuma raya karkara a cikin shekaru goman da suka wuce.

A shekarun baya dai lokacin da na samu damar kai ziyara kasar Sin a yayin da na je wasu larduna wadanda suka hada da Beijing, da Shanghai, da Anhui, da Jiangsu, da Fujian, da Shaanxi.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Abubuwan da suka fi burge ni a shirin yaki da fatara na kasar Sin a nan shi ne kokarin da samari da suka kammala karatun jami’o’i suke yi a kan wani shiri wanda aka dauka su domin aiki da taimakawa a kauyuka don ganin iyalai masu fatara su samu kudaden shiga ta hanyoyi da dama musamman noma, da kiwon dabbobi, da sana’o’i domin fitar da su daga kuncin fatara.

Wani abun burgewar kuma da na lura da shi a cikin ziyarce-ziyarce na a cikin kasar shi ne wato, manoma ba su biyan kudi a manyan hanyoyi wato “toll gate” in dai har sun dauko kayan amfanin gona. Suna wucwe ne kyauta, kuma wannan duk yana cikin tsarin tallafi da rage fatara ne.
Bugu da kari, a sakamakon wannan nauyi da jam’iyyar Kwaminis ta kasar ta dauka, an samu cimma nasarar saukaka fatara da kuma bunkasa yankunan karkara a gomman shekarun da suka gabata a karkashin shirin, wanda aka ayyana a taro na kasa na 18 na jam’iyyar Kwaminis ta kasar a shekarar 2012.

A wannan lokaci ne aka kaddamar da shirin kuma aka tashi gaba daya domin cimma nasarar kakkabe fatara wanda a karshe aka yi nasarar fitar da mutanen da talaucin ya yi ma katutu fiye da miliyan 100. A nan dai ina iya cewa samar da abinci ta fannin fadada harkar noma da raya karkara ne babbar nasara domin a yau, kasar Sin tana ci da kanta duk da tana da yawan mutanen da ya kai biliyan 1.4, dan haka kuma ana samun karin ci gaba a kauyuka.

A sakamakon nasarar da kasar Sin ta samu na cimma burinta na kawar da talauci da raya karkara, kasashen Afirka ma za su iya koyi da matakan da kasar Sin ta dauka domin saukaka fatara a kasashensu.

A Najeriya, a misali, gwamnati ta dauki irin wannan darasi a yayin da ta bullo da shirin bunkasa noman shinkafa ta hanyar bayar da basussuka masu karamar riba da tallafi ga manoma ta hanyar samar da kayan aikin gona da takin zamani. Ta wannan darasi, manoma da dama sun samu ci gaba kuma kasar Najeriya ta samu bunkasar tattalin arziki da kuma rage kudin fita da ake amfani da su wajen shigowa da shinkafar a shekarun baya. (Mai sharhi: Lawal Sale)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalaman Xi Jinping Game Da Kishin Kasa

Next Post

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

2 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

3 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

5 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

5 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

7 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

7 hours ago
Next Post
Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

LABARAI MASU NASABA

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.