• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarau Ya Fara Jagorantar Sabuwar Tafiyar Kawo Sauyi A Nijeriya

by Sadiq
12 months ago
Shekarau

Tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya fara jagorantar wata tafiya domin samar da shugabanci na gari a Nijeriya.

Wata tawaga da ya jagoranta zuwa Abeokuta ta ziyarci tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da tsohon ministan tsaro, Theophilus Yakubu Danjuma, domin neman shawarwari kan manufarsu.

  • Yadda Dortmund Ta Barar Da Garinta A Santiago
  • Cike Giɓin Ababen More Rayuwa: Nijeriya Na Buƙatar Dala Tiriliyan 3 A Cikin Shekara 30 – Kakakin Majalisa

A yayin ziyarar, tsohon gwamnan na Kano, ya shaida wa manema labarai cewa babban dalilin da ya sa suka fara tuntubar masu ruwa da tsaki shi ne, nemo wa kasar mafita.

Shekarau, ya ce a cikin tafiyar da suka fara suna son su zaburar da al’umma tun daga matakin mazaba har zuwa matakin kasa domin su gano wadanda za su yi musu adalci idan suka ba su shugabanci a Nijeriya.

“Ba mu ce mun fi kowa iyawa ba, amma mun yarda cewa a Arewa da kuma kasar nan baki daya muna da nagartatttun mutane wadanda idan aka ba su dama, za mu zaburar da al’umma domin su hango duk wanda suka san yana da wata gogewa da adalci da kuma gaskiyar da zai jagoranci mutane da adalci, domin mu yi yunkuri mu tallata su, mu fito da su a ba su dama su zo su gabatar da abin da suke yi.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

“A yadda ake tafiya an mayar da siyasa ta zama ta kudi, ta zama ta ubangida, suna dora mutane shugabanci ko sun iya, ko ba su iya ba, ko sun dace, ko ba su dace ba, ko suna da kwarewa ko ba su da ita, kuma duk yadda suka dama haka ake sha,” in ji shi.

Shekarau, ya ce suna son su zaburar da ‘yan kasa daga Arewa da ke da kuri’a mafi yawa da ma kasa baki daya su daina la’akari da abin da ake ba su ranar zabe ta yadda wasu ke dasa shugabannin da ba su dace ba.

Kazalika, ya ce za su nemi hadin kan duk wanda yake son bayar da gudunmawa kuma za su samu nasara.

Ya ce babbar manufarsu ita ce a samar da shugabanci na gari a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Next Post
Gidauniya Da Gwamnatin Zamfara Sun Tallafa Wa Mata 200 Da Kajin Kiwo

Gidauniya Da Gwamnatin Zamfara Sun Tallafa Wa Mata 200 Da Kajin Kiwo

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.