• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Kananan Hukumomi: Kallo Ya Koma Kan Gwamnatin Tarayya Wajen Aiwatar Da Hukuncin Kotun Koli

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yancin Kananan Hukumomi: Kallo Ya Koma Kan Gwamnatin Tarayya Wajen Aiwatar Da Hukuncin Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rudani kan ayyukkan hadakar kwamitin ma’aikatu da gwamnatin tarayya ta kafa domin aiwatar da hukuncin da kotun koli wacce ta yanke na bai wa kananan hukumomi 774 ‘yancin cin gashin kansu.

Wasu shugabannin kungiyar kananan hukumomin Nijeriya (ALGON), sun ce suna jiran hadakar kwamitin ma’aikatun ya bayyana samfurin yadda za a aiwatar da shirin.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Kafa kwamitin mai mutum 10 tare da sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, ya biyo bayan umarnin kotun koli na cewa kwamitin rarraba assun gwamnatin tarayya (FAAC) ya bayar da kudaden kai tsaye ga kananan hukumomin.

Kotun kolin ta kuma bayyana cewa ya saba wa tsarin mulki gwamnonin jihohi su rike kudaden da aka ware don gudanar da ayyukan kananan hukumomi.

Yayin da gwamnati ta yi gum kan wa’adin da aka bai wa kwamitin na gudanar da aikinsa, ana sa ran gwamnati tarayya za ta gaggauta daukar mataki kan wa’adin tun da kotun koli ta ba da umarnin daukar matakin gaggawa kan bai wa kananan hukumomin ‘yancin cin gashin kansu.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Wasu shugabannin kungiyar ta ALGON, sun shaida wa manema labarai cewa mambobin kungiyar sun damu kan jinkirin da kwamitin ke yi na kammala aikin da aka dora masa domin zartar da hukunci kotun koli.

Shugabannin kungiyan sun ce sun dauki matakan da suka dace don shirya taron manema labarai da zarar kwamitin ya bayyana shawararsa.

Rahotannin sun nuna cewa za a fara aiwatar da shirin ne a farkon watan Oktoba, yayin da gwamnatocin jihohi suka yi yunkurin shirya zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli domin cika tafarkin dimokuradiyya.

Jihohin Kaduna, Ribas, Bauchi, Benuwai, Imo, Kwara, Filato, Inugu, Abiya, Ebonyi, Kebbi, Sakkwoto da Akwa Ibom na daga cikin jihohin da suka yi zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansiloli.

Jihohin Katsina da Kano da Ogun da Osun da kuma Anambra suna cikin jerin jahohin da su ma ke shirin gudanar da zaben kananan hukumomi.

A ranar 24 ga watan Agusta ne aka kaddamar da mambobin hadakar kwamitin ma’aikatun domin aiwatar da hukuncin kotun koli wadada sun hada da SGF, Sanata George Akume a matsayin shugaba; ministan kudi; babban lauyan gwamnatin tarayya; ministan kasafi da tsare-tsare tattalin arziki; akanta janar na tarayya; gwamnan Babban Bankin Nijeriya; babban sakataren ma’aikatar kudi ta tarayya; shugaban hukumar rarraba kudaden haraji na kasa; wakilin gwamnonin jihohi da kuma wakilin kananan hukumomi.

Babban aikin kwamitin a cewar ofishin SGF shi ne, tabbatar da cewa an bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kansu, ta yadda za su yi aiki yadda ya kamata ba tare da tsangwama daga gwamnatocin jihohi ba.

Ya kara da cewa matakin ya yi daidai da kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu na ganin an aiwatar da tsarin da ya dace a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan, wanda ya amince da kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnati.

Gwamnatin tarayya ta bakin ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi ta maka jihohi 36 a gaban kotu bisa zarginsu da amfani da kudaden da aka ware wa kananan hukumomin a cikin asusun hadin gwiwa na jihohi da na kananan hukumomi.

A bisa dalilan da hukumomin tarayya suka gabatar tare da shaidu, kotun a hukuncin da ta yanke ta bayyana cewa ba bisa ka’ida ba ne gwamnonin jihohi su rike amfani da kudaden kananan hukumomi.

A kwanakin baya, ministan shari’a ya yi kira ga manyan lauyoyin kasar nan da su shawarci gwamnonin jihohi da su yi biyayya ga hukuncin da kotun koli ta yanke game da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi a Nijeriya.

Fagbemi, a wani taro da aka gudanar a Abuja, ya kuma gargadi shugabannin kananan hukumomin da su yi amfani da kudaden da aka ware masu ta hanyar da ta dace domin su ba gwamnonin jihohinsu ba ne za a tuhuma idan suka gaza.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta dauki matakin ne wajen tafiyar da kananan hukumomin ta hannun shugabannisu sabanin gwamnoni.

A jawabinsa na bikin murnar cikar Nijeriya shekaru 64 da samun ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, Shugaba Bola Tinubu ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin tarayya za ta aiwatar da hukuncin da kotun kolin ta yanke wanda ta ba da ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi 774 na kasar nan a matsayin wani bangare na matakan da za a dauka domin inganta tattalin arziki.

A yanzu haka dai kallo ya koma kan gwamnatin tarayya wajen aiwatar da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YanciKananan HukumomiZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Next Post

A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

LABARAI MASU NASABA

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.