ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Kananan Hukumomi: Kallo Ya Koma Kan Gwamnatin Tarayya Wajen Aiwatar Da Hukuncin Kotun Koli

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Hukumomi

An samu rudani kan ayyukkan hadakar kwamitin ma’aikatu da gwamnatin tarayya ta kafa domin aiwatar da hukuncin da kotun koli wacce ta yanke na bai wa kananan hukumomi 774 ‘yancin cin gashin kansu.

Wasu shugabannin kungiyar kananan hukumomin Nijeriya (ALGON), sun ce suna jiran hadakar kwamitin ma’aikatun ya bayyana samfurin yadda za a aiwatar da shirin.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Kafa kwamitin mai mutum 10 tare da sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, ya biyo bayan umarnin kotun koli na cewa kwamitin rarraba assun gwamnatin tarayya (FAAC) ya bayar da kudaden kai tsaye ga kananan hukumomin.

ADVERTISEMENT

Kotun kolin ta kuma bayyana cewa ya saba wa tsarin mulki gwamnonin jihohi su rike kudaden da aka ware don gudanar da ayyukan kananan hukumomi.

Yayin da gwamnati ta yi gum kan wa’adin da aka bai wa kwamitin na gudanar da aikinsa, ana sa ran gwamnati tarayya za ta gaggauta daukar mataki kan wa’adin tun da kotun koli ta ba da umarnin daukar matakin gaggawa kan bai wa kananan hukumomin ‘yancin cin gashin kansu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Wasu shugabannin kungiyar ta ALGON, sun shaida wa manema labarai cewa mambobin kungiyar sun damu kan jinkirin da kwamitin ke yi na kammala aikin da aka dora masa domin zartar da hukunci kotun koli.

Shugabannin kungiyan sun ce sun dauki matakan da suka dace don shirya taron manema labarai da zarar kwamitin ya bayyana shawararsa.

Rahotannin sun nuna cewa za a fara aiwatar da shirin ne a farkon watan Oktoba, yayin da gwamnatocin jihohi suka yi yunkurin shirya zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli domin cika tafarkin dimokuradiyya.

Jihohin Kaduna, Ribas, Bauchi, Benuwai, Imo, Kwara, Filato, Inugu, Abiya, Ebonyi, Kebbi, Sakkwoto da Akwa Ibom na daga cikin jihohin da suka yi zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansiloli.

Jihohin Katsina da Kano da Ogun da Osun da kuma Anambra suna cikin jerin jahohin da su ma ke shirin gudanar da zaben kananan hukumomi.

A ranar 24 ga watan Agusta ne aka kaddamar da mambobin hadakar kwamitin ma’aikatun domin aiwatar da hukuncin kotun koli wadada sun hada da SGF, Sanata George Akume a matsayin shugaba; ministan kudi; babban lauyan gwamnatin tarayya; ministan kasafi da tsare-tsare tattalin arziki; akanta janar na tarayya; gwamnan Babban Bankin Nijeriya; babban sakataren ma’aikatar kudi ta tarayya; shugaban hukumar rarraba kudaden haraji na kasa; wakilin gwamnonin jihohi da kuma wakilin kananan hukumomi.

Babban aikin kwamitin a cewar ofishin SGF shi ne, tabbatar da cewa an bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kansu, ta yadda za su yi aiki yadda ya kamata ba tare da tsangwama daga gwamnatocin jihohi ba.

Ya kara da cewa matakin ya yi daidai da kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu na ganin an aiwatar da tsarin da ya dace a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan, wanda ya amince da kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnati.

Gwamnatin tarayya ta bakin ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi ta maka jihohi 36 a gaban kotu bisa zarginsu da amfani da kudaden da aka ware wa kananan hukumomin a cikin asusun hadin gwiwa na jihohi da na kananan hukumomi.

A bisa dalilan da hukumomin tarayya suka gabatar tare da shaidu, kotun a hukuncin da ta yanke ta bayyana cewa ba bisa ka’ida ba ne gwamnonin jihohi su rike amfani da kudaden kananan hukumomi.

A kwanakin baya, ministan shari’a ya yi kira ga manyan lauyoyin kasar nan da su shawarci gwamnonin jihohi da su yi biyayya ga hukuncin da kotun koli ta yanke game da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi a Nijeriya.

Fagbemi, a wani taro da aka gudanar a Abuja, ya kuma gargadi shugabannin kananan hukumomin da su yi amfani da kudaden da aka ware masu ta hanyar da ta dace domin su ba gwamnonin jihohinsu ba ne za a tuhuma idan suka gaza.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta dauki matakin ne wajen tafiyar da kananan hukumomin ta hannun shugabannisu sabanin gwamnoni.

A jawabinsa na bikin murnar cikar Nijeriya shekaru 64 da samun ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, Shugaba Bola Tinubu ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin tarayya za ta aiwatar da hukuncin da kotun kolin ta yanke wanda ta ba da ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi 774 na kasar nan a matsayin wani bangare na matakan da za a dauka domin inganta tattalin arziki.

A yanzu haka dai kallo ya koma kan gwamnatin tarayya wajen aiwatar da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai.

Hukumomi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

A Karon Farko Yawan Hatsi Da Sin Za Ta Samar Zai Kai Ton Miliyan 700 A Bana

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.