• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

by Hussein Yero and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da bayar da goyon baya ga ayyukan soji a jihar.

 

A ranar Alhamis ɗin nan ne ministan ya ziyarci gidan gwamnatin Zamfara da hedikwatar rundunar haɗin gwiwa ta ‘Operation Fansar Yamma’ da ke Gusau.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran
  • TCN Ta Gano Dalilin Katsewar Wutar Lantarki A Arewacin Nijeriya, Ta Fara Gyara

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ziyarar na da nufin inganta haɗin gwiwa tsakanin jihar da ma’aikatar tsaro.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan ya tattauna batutuwan da suka shafi ziyarar da gwamna Lawal da gwamna Raɗɗa suka kai Ma’aikatar Tsaro a farkon makon nan.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na bayar da haɗin kai ga dukkanin hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Zamfara.

 

“Ina so in miƙa godiyata ga Ministan Tsaro, wanda ya zo yau domin tattauna batun matsalar tsaro a Zamfara.

 

“Kwanaki kaɗan da suka gabata ni da gwamnan jihar Katsina muka je ofishin minista a Ma’aikatar Tsaro, inda muka tattauna batutuwa masu muhimmanci.

 

“Bayan kwana biyu, ministan ya zo wurinmu. Wannan abin a yaba ne na irin ƙwazon da ministan ya nuna.

 

“Zamfara na fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, amma a matsayinmu na gwamnati mai cikakken iko, duk mun tashi tsaye don neman taimako da haɗa kai da hukumomin tsaro. Mun himmatu wajen ba da dukan taimako ga sojoji.

 

“Za mu kai yaƙi ne ga ‘yan bindigar saboda kare kanmu. Abin da na gani zuwa yanzu ya nuna cewa batun ‘yan bindiga zai zama tarihi in Allah Ya yarda.

 

“Na yi alƙawari ga ministan. Bugu da ƙari, na saya wa sojoji motocin da harsashi ba ya fasa su guda goma. Haka kuma akwai sauran kayan aikin da za a ba jami’an tsaro domin taimaka musu wajen yaƙar ‘yan bindiga.

 

“Idan za mu iya magance ƙalubalen ‘yan bindiga a Zamfara, za a magance kashi 90 na matsalar jihar.

 

“Ina kira ga jami’an tsaro, musamman sojoji, cewa muna buƙatar su. Ina da yaƙinin suna da abin da ake buƙata don kawar da ‘yan ta’adda.

 

“Na yi alƙawari, kuma ina tare da ku. Ina godiya ga kowa da kowa, musamman Minista da ke ba da lokacin zama tare da mu.”

 

A farko dai, Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ‘yan bindiga na da alaƙa da ci gaba da goyon bayan gwamnatin Gwamna Lawal.

 

“Mun fara ganin an samu ci gaba, sakamakon goyon bayan Gwamnan Jihar Zamfara.

 

“Gwamnan ya samar da masauki ga kwamandojin soji, wuraren horo, kyamarori masu sa ido na nesa, motoci, da dai sairan kayan aiki. Har ma ya bai wa sojojin motocin yaƙi. Ranka ya daɗe, mun gode maka sosai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran

Next Post

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

51 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.