• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jinjina Wa Obaseki Kan Shirin Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Edo 

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Jinjina Wa Obaseki Kan Shirin Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Edo 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa Gwamna Godwin Obaseki kan yadda ya kawo sauyi da kuma ƙudirinsa na inganta fannin kiwon lafiya a Jihar Edo.

 

Gwamnan ya kasance babban baƙo a wajen bikin ƙaddamarwa, rantsar da sababbin ɗalibai da kuma cika shekaru 60 da kafa Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya da Fasaha ta Edo (EdoCOHEST) da aka gudanar a birnin Benin a ranar Larabar da ta gabata.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Da Ministoci 7 Da Tinubu Ya Nada
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa bayan ƙaddamar da kwalejin, gwamnonin sun zagaya da kayayyakin zamani da aka samar a ginin.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

A lokacin da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Lawal ya ba da shawarar cewa jihohin biyu su kafa shirin musayar ɗalibai, wanda zai bai wa ɗalibai mata da ke makarantun kiwon lafiya a Zamfara damar zuwa kwalejin Edo domin yin wani zagon karatu.

Gwamna lawal

Ya ce, “Haƙiƙa babban abin alfahari ne da kuma gata kasancewata a nan wurin tare da ɗan uwana da mutanen kirki na jihar Edo don buɗe wani sabon babi na Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiyar da Fasaha ta Edo, musamman ga ɗaliban da suka shigo yanzu.

 

“Yayin da muka taru a nan, ina jinjina irin hangen nesa da jajircewar ɗan uwana Gwamna Obaseki, wanda ya sake farfaɗo da fata a Jihar Edo cikin kyakkyawar manufa, za a iya samun ɗaukaka duk da rashin daidaito a ƙasarmu mai albarka.

 

“Lokacin da na samu bayanai game da wannan ingantaccen aikin gaba ɗaya, na yaba kuma na jinjina wa ɗan uwana kan irin wannan manufa da za a iya cimmawa kaɗai ta bangaren juriya, hangen nesa da sadaukarwa.

 

“Ga ɗaliban da suka shigo a yau, zan ce ku ne burinmu kuma alfaharinmu. Kuna wakiltar jihar Edo da ƙasar mu gaba ɗaya ne. Don haka kada ku iyakance kanka.

 

“Ku yi karatu kuma ku yi fice a karatun; ku daraja aikin da ɗan uwana ya yi a yau don kanku da ɗalibai a nan gaba.

Gwamna lawal

“Baya ga samar da ƙwararrun masana kiwon lafiya, ina addu’a cewa wannan kwaleji ta zama wata gada ta haɗa kan jama’a, samar da ayyukan yi, da bunƙasar tattalin arziki a ciki da wajen jihar Edo. ”

 

Gwamna Obaseki ya gode wa Gwamna Lawal bisa girmama gayyatar da mutanen jihar Edo suka yi masa.

 

“Ina matuƙar godiya da kai ɗan uwana Gwamnan Jihar Zamfara, Dokta Dauda Lawal da ka zo min wannan biki mai bangarori uku, wanda ya hada da ƙaddamarwa, rantsar da sabbin ɗalibai, da kuma cika shekaru 60 da kafa Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya da Fasaha ta Edo (EdoCOHEST).”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwon LafiyaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume

Next Post

Gwamna Sani Ya Amince Da ₦72,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Jihar Kaduna 

Related

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

17 hours ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

19 hours ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

23 hours ago
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

1 day ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

2 days ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

2 days ago
Next Post
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Amince Da ₦72,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Jihar Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

May 31, 2025
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

May 31, 2025
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.