ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

by Sadiq
9 months ago
DSS

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta gurfanar da manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, a gaban Kotun Ƙoli ta Tarayya da ke Abuja a ranar Laraba.

Mutanen su ne Mahmud Usman (wanda ake kira Abu Bara’a Abbas ko Mukhtar) da mataimakinsa, Mahmud Al-Nigeri (wanda aka fi sani da Malam Mamuda).

  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata
  • Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Ana tuhumar su da zarge-zarge 32 da suka shafi ta’addanci a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite.

ADVERTISEMENT

DSS ta ce waɗannan mutane ne suka kai harin gidan yarin Kuje a watan Yulin 2022, wanda ya bai wa fursunoni sama da 600 damar tserewa.

Haka kuma, ana tuhumar su da kitsa kai harin sansanin sojin Nijeriya na Wawa a Jihar Neja a 2022, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

DSS ta ce, shugabannin sun samu horo na musamman a kan amfani da makamai, dabarun yaƙi da kuma ƙera bama-bamai a ƙasashen Mali da Libya.

Ta ce Mamuda ya samu horo na musamman daga malamai masu tsattsauran ra’ayi a tsakanin 2013 da 2015.

Hakazalika, suna da hannu a sace manyan mutane, ciki har da sace wani Injiniya ɗan ƙasar Faransa, Francis Collomp a 2013 da kuma sace Alhaji Musa Umar Uba, Magajin Garin Daura a 2019.

Ana kuma zarginsu da fashi da makami da kuma shirin kai hari wajen wani haƙar uranium a Nijar, wanda shirin nasu bai yi nasara ba.

Mai Bai wa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu ne, ya tabbatar da kama su yayin wani samamen haɗin gwiwa da jami’an tsaro suka kai.

Ribadu ya ce kama su zai kawo wa shugabancin ƙungiyar ta Ansaru koma baya.

Ansaru ta ɓalle daga cikin Boko Haram a 2012, inda da farko ta bayyana kanta a matsayin ƙungiya mai “tausaya wa al’umma.”

Amma daga baya ta haɗu da ƙungiyoyin ta’addanci na ƙasa da ƙasa, har ta ɗauki tambarin Al-Qaeda.

MASU ALAKA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar
Manyan Labarai

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.