ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

by Ra'ayinmu
12 months ago
Nijeriya

Bisa wasu alƙaluma da Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa da ke aikin jin ƙai wato Red Cross ta fitar a kwanan baya, sun nuna cewa, aƙalla ƴan Nijeriya dubu 23,659 ne suka ɓace, waɗanda kuma har yau, ƴanuwansu ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Wannan lamari ke ci gaba da jefa rayuwar ƴanuwa aƙalla dubu 13,595 a cikin fargaba.

A saboda hakan, ake ganin ya zama wajibi matakan gwamnati uku na ƙasar su gaggauta ɗaukar matakan gaggawa domin a lalubo mafita. Red Cross ta fitar da waɗannan alƙaluman ne a yayin zagayowar ranar ɓacewar mutane ta duniya da aka gudanar a baya-bayan nan. Ƙungiyar ta yi nuni da cewa, batun ya fi ƙarfin alƙaluma, domin irin halin damuwa da iyaye mata da ƴaƴansu ke shiga musamman sakamakon hare-haren ƴan ta’adda.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi
  • An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

Kazalika, tafiye-tafiyen ƴan cinari a ciki da wajen ƙasar na ƙara haifar da ɓacewar mutane wanda hakan ya janyo mutuwarsu, ƴanuwansu kuma ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Idan da gawar aka gani, hakan na sauƙaƙa wa iyali maimakon a ce sun ɓace gaba ɗaya. Batun kuma ba wai kawai ya tsaya kan waɗanda suka rasa ƴanuwansu ba, hatta al’umma gaba ɗaya na shiga cikin tsoro mai yuwa su fuskanci irin wannan matsala.

ADVERTISEMENT

Matakan da gwamnati ke ɗauka kan lamarin sun yi ƙaranci. Ko da yake hukumomin tsaro na fitar da sanarwar ceto wasu daga cikin mutanen da suka ɓace, yawan ɓacewar mutane ya sa ya zama wajibi a ɗauki tsare-tsaren da za su magance wannan matsala. Har yanzu babu wani ingantaccen tsari na ƙasa da aka samar domin magance matsalar, balle a ware kuɗaɗe don tallafa wa ƴan uwa da lamarin ya shafa.

Ƴanuwan da ke kai rahoton ɓacewar mutanensu kuma suna fuskantar ɓata lokaci saboda tsararan tsare-tsare, abin da ke hana su samar da bayanan da suka kamata. Sai dai ƙungiyoyi kamar ICRC sun samar da tsarin zamani kan lamarin, wanda ya ba su damar gano wasu da suka ɓace tare da miƙa su ga iyalansu, har ma da tattara sabbin sunaye 451 na waɗanda suka ɓace. Amma bai kamata a bar irin waɗannan ƙungiyoyi kaɗai da nauyin ba, domin abu ne da gwamnati itama ta kamata ta ɗauki nauyi.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

Ya kamata a kafa hukumar musamman da za ta kula da gano mutane da suka ɓace tare da bata ƙarfi don gudanar da bincike. Kaso 68 cikin 100 na masu neman ƴaƴan da suka ɓace iyaye mata ne, amma da dama suna dawowa hannu rabbana saboda rashin tsari daga mahukunta. A jihar Yobe kaɗai, yara 2,500 ne aka ce sun ɓace, mafi yawan su a Gujba, abin da ya nuna gazawar gwamnati wajen kare rayuka a Arewa maso Gabas.

Yakuma zama wajibi a samar da tsare-tsaren gwamnati da za su kare haƙƙin ƴanuwa waɗanda suka rasa nasu, musamman a jihohin da ake fama da tashe-tashen hankula. Waɗannan tsare-tsaren za su yi aiki kaf shoulder da al’ummomin yankuna, sarakunan gargajiya, malaman addini da ƙungiyoyin sa kai.

Haka kuma dole al’umma su tsaya tsayin daka wajen bai wa iyalan waɗanda suka ɓace kariya daga nuna masu ƙyama tare da taimaka musu da tallafin da suke matuƙar buƙata.

Nijeriya
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Next Post
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.