ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

by Ra'ayinmu
10 months ago
Nijeriya

Bisa wasu alƙaluma da Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa da ke aikin jin ƙai wato Red Cross ta fitar a kwanan baya, sun nuna cewa, aƙalla ƴan Nijeriya dubu 23,659 ne suka ɓace, waɗanda kuma har yau, ƴanuwansu ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Wannan lamari ke ci gaba da jefa rayuwar ƴanuwa aƙalla dubu 13,595 a cikin fargaba.

A saboda hakan, ake ganin ya zama wajibi matakan gwamnati uku na ƙasar su gaggauta ɗaukar matakan gaggawa domin a lalubo mafita. Red Cross ta fitar da waɗannan alƙaluman ne a yayin zagayowar ranar ɓacewar mutane ta duniya da aka gudanar a baya-bayan nan. Ƙungiyar ta yi nuni da cewa, batun ya fi ƙarfin alƙaluma, domin irin halin damuwa da iyaye mata da ƴaƴansu ke shiga musamman sakamakon hare-haren ƴan ta’adda.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi
  • An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

Kazalika, tafiye-tafiyen ƴan cinari a ciki da wajen ƙasar na ƙara haifar da ɓacewar mutane wanda hakan ya janyo mutuwarsu, ƴanuwansu kuma ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Idan da gawar aka gani, hakan na sauƙaƙa wa iyali maimakon a ce sun ɓace gaba ɗaya. Batun kuma ba wai kawai ya tsaya kan waɗanda suka rasa ƴanuwansu ba, hatta al’umma gaba ɗaya na shiga cikin tsoro mai yuwa su fuskanci irin wannan matsala.

ADVERTISEMENT

Matakan da gwamnati ke ɗauka kan lamarin sun yi ƙaranci. Ko da yake hukumomin tsaro na fitar da sanarwar ceto wasu daga cikin mutanen da suka ɓace, yawan ɓacewar mutane ya sa ya zama wajibi a ɗauki tsare-tsaren da za su magance wannan matsala. Har yanzu babu wani ingantaccen tsari na ƙasa da aka samar domin magance matsalar, balle a ware kuɗaɗe don tallafa wa ƴan uwa da lamarin ya shafa.

Ƴanuwan da ke kai rahoton ɓacewar mutanensu kuma suna fuskantar ɓata lokaci saboda tsararan tsare-tsare, abin da ke hana su samar da bayanan da suka kamata. Sai dai ƙungiyoyi kamar ICRC sun samar da tsarin zamani kan lamarin, wanda ya ba su damar gano wasu da suka ɓace tare da miƙa su ga iyalansu, har ma da tattara sabbin sunaye 451 na waɗanda suka ɓace. Amma bai kamata a bar irin waɗannan ƙungiyoyi kaɗai da nauyin ba, domin abu ne da gwamnati itama ta kamata ta ɗauki nauyi.

LABARAI MASU NASABA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Ya kamata a kafa hukumar musamman da za ta kula da gano mutane da suka ɓace tare da bata ƙarfi don gudanar da bincike. Kaso 68 cikin 100 na masu neman ƴaƴan da suka ɓace iyaye mata ne, amma da dama suna dawowa hannu rabbana saboda rashin tsari daga mahukunta. A jihar Yobe kaɗai, yara 2,500 ne aka ce sun ɓace, mafi yawan su a Gujba, abin da ya nuna gazawar gwamnati wajen kare rayuka a Arewa maso Gabas.

Yakuma zama wajibi a samar da tsare-tsaren gwamnati da za su kare haƙƙin ƴanuwa waɗanda suka rasa nasu, musamman a jihohin da ake fama da tashe-tashen hankula. Waɗannan tsare-tsaren za su yi aiki kaf shoulder da al’ummomin yankuna, sarakunan gargajiya, malaman addini da ƙungiyoyin sa kai.

Haka kuma dole al’umma su tsaya tsayin daka wajen bai wa iyalan waɗanda suka ɓace kariya daga nuna masu ƙyama tare da taimaka musu da tallafin da suke matuƙar buƙata.

Nijeriya
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

MASU ALAKA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare
Labarai

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Next Post
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.