• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ce Ta Fi Tsadar Tafiyar Da Gwamnati A Afirka -RMAFC

by Shehu Yahaya
8 months ago
in Labarai
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar raba kudaden shiga da hada-hadar kudi ta Nijeriya (RMAFC) ta koka kan tsadar harkokin mulki a Nijeriya tsawon shekaru, tana mai cewa Nijeriya ce mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka tafi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnata.

Hukumar ta ce lamarin da ke da ban tsoro da rashin dorewa kan yadda jama’a ke nuna damuwa da tattaunawa saboda mummunan tasirinsa da ke janyo wa bangaren zuba jari, fadada masana’antu da samar da ababen more rayuwa, da kuma ci gaban hakikanin fannin tattalin arziki.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Manjo Janar Olufemi MuÆ™addashin Babban Hafsan Sojin Ƙasa

Shugaban hukumar, Dakta Muhammad Bello, shi ne ya bayyana haka a Abuja, inda ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa umarnin da ya bayar na rage yawan ayarin ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa a matsayin hanyar rage tsadar tafiyar da gwamnati, yayin da ya bukaci gwamnatocin jihohi su ma su yi koyi da shi.

Ya yi kira da a rage yawan masu rike da mukaman siyasa kamar yadda aka ba da shawarar a cikin kunshin biyan albashi na RMAFC, na masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati da kuma tabbatar da yadda ake kashe kudaden gwamnati a kowane mataki.

Shugaban RMAFC ya ce, “Shaidu sun nuna cewa Nijeriya ce kasa wacce aka fi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnati a duk kasashen da suke Afirka. Hukumar ta fito fili ta bayyana matsayarta kan wannan batu ta hanyar gabatar da takarda.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

“A bayyane yake cewa farashin mulkin Nijeriya yana daya daga cikin mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka, wanda ya kawo cikas ga gwamnati wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta kamar su raya ababen more rayuwa, samar da ingantaccen kiwon lafiya, inganta harkokin ilimi da dai sauransu.”

Dakta Shehu ya ce matakin zai taimaka matuka wajen rage tsadar harkokin mulki, wanda wani bangare ne ke da alhakkin rage samar da ababen more rayuwa da walwala da faduwar zuba jari da rashin aikin yi da karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Ya kara da cewa babu wata al’umma da za ta iya samun ci gaba mai ma’ana, sai dai idan ta samar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’amura gwamnati da za su iya amfani da albarkatun kasa domin amfanin kowa.

Ya ce hukumar RMAFC ta yi shekaru da yawa tana yaki da lamarin, ba wai kawai ta bayar da shawarar rage farashin mulki ba ne a matsayin hanyar tadanar kudade, sannan kuma ta ba da shawarwari masu yawa ga gwamnati a dukkan matakai kan tsarin bukatar rage yawan kashe kudin da ba dole ba da kuma lura da kashe kudi kan ayyukan ci gaba wadanda za su yi tasiri mai kyau ga rayuwar ‘yan kasa.

A cewarsa, tsadar harkokin mulki a Nijeriya ya samo asali ne sakamakon tsadar manyan ofisoshi, da yawan ma’aikatun da hukumomin gwamnati da kuma cin hanci da rashawa.

“Sauran abubuwan sun hada da tsadar ayyukan gwamnati sakamakon gazawar ababen more rayuwa, tsadar tsaro sakamakon ta da kayan baya, garkuwa da mutane da ta da kayan baya da kuma fashi da makami, yawan albashi da alawus alawus, almubazzaranci da ayyuka da kashe kudade, dimbin basussuka na gida da waje da kuma raunin cibiyoyin tilasta aiwatarwa da ayyuka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaNijeriyaTsadar Raywa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

Next Post

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

3 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

5 hours ago
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

10 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

12 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

12 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

12 hours ago
Next Post
Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.