• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga kafafen yaɗa labaran Nijeriya da kada su yi ƙasa a gwiwa wajen kare dimokuraɗiyyar ƙasar da aka kwashe shekaru 24 ana yi.

 

Ministan ya jaddada hakan ne a wata ziyarar ban girma da Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) ta kai masa a ofishinsa domin tattaunawa kan shirye-shiryen Babban Taron Editocin Nijeriya (ANEC) karo na 20, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 6-9 ga Nuwamba, 2024, a Yenagoa, Jihar Bayelsa.

  • Dauke Lantarkin Arewa
  • Tawagar Likitocin Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Aikin Jinya Ga Asibitin Tanzaniya

Idris ya jaddada muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen tallafawa tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda ya tuna da muhimmiyar rawar da suka taka a gwagwarmaya da mulkin kama-karya na sojoji.

 

Labarai Masu Nasaba

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

“Kowa ya yi gwagwarmaya sosai a tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda kafafen yaɗa labarai ke kan gaba wajen yaƙi da mulkin kama-karya na soji.

 

“Saboda haka, shekaru 24 bayan haka, bai kamata a ga kafafen yaɗa labarai sun yi ƙasa a gwiwa ba a wannan muhimmin lokaci. Abin da ya kamata su yi shi ne ci gaba da ƙarfafa goyon bayansu ga dimokuraɗiyya.”

 

Ministan ya tabbatar wa shugabannin NGE, ƙarƙashin jagorancin Shugaban NGE, Eze Anaba, kan ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare martabar dimokraɗiyya, gami da ‘yancin yaɗa labarai.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai da su zama jagororin kare dimokuraɗiyyar Nijeriya, da inganta zaman lafiya, haɗin kai, da tsaron ƙasa wajen yaɗa lamuran ƙasa.

 

Idris ya ci gaba da bayyana cewa ajandar kawo sauyi na gwamnatin Tinubu na ci gaba da gudana, ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su bayyana abubuwa masu kyau, yana mai cewa Nijeriya na kan hanyar zuwa wani sabon zamani na ci gaban zamantakewa da tattalin arziƙi, wanda ke zuwa da ƙalubale.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren yaɗa labarai ta hanyar ayyuka na musamman kamar bayar da lamuni ta Bankin Masana’antu da magance tsadar buga jaridu.

 

A nasa jawabin, Anaba ya bayyana muhimmancin taron ANEC da ke tafe a Jihar Bayelsa, inda ya bayyana cewa takensa, “Haɓaka Tattalin Arziƙi da Dabarun Ci Gaba a Ƙasa Mai Ɗimbin Albarkatu,” ya yi daidai da buƙatun da Nijeriya ke da shi a halin yanzu da kuma buƙatar neman mafita don samar da ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote

Next Post

Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina
Labarai

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

7 minutes ago
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su
Labarai

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

2 hours ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

3 hours ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

10 hours ago
Gwamna Yusuf
Labarai

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

12 hours ago
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya
Manyan Labarai

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

13 hours ago
Next Post
Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

September 3, 2025
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

September 3, 2025
Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

September 3, 2025
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

September 3, 2025
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

September 3, 2025
Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.