ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga kafafen yaɗa labaran Nijeriya da kada su yi ƙasa a gwiwa wajen kare dimokuraɗiyyar ƙasar da aka kwashe shekaru 24 ana yi.

 

Ministan ya jaddada hakan ne a wata ziyarar ban girma da Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) ta kai masa a ofishinsa domin tattaunawa kan shirye-shiryen Babban Taron Editocin Nijeriya (ANEC) karo na 20, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 6-9 ga Nuwamba, 2024, a Yenagoa, Jihar Bayelsa.

ADVERTISEMENT
  • Dauke Lantarkin Arewa
  • Tawagar Likitocin Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Aikin Jinya Ga Asibitin Tanzaniya

Idris ya jaddada muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen tallafawa tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda ya tuna da muhimmiyar rawar da suka taka a gwagwarmaya da mulkin kama-karya na sojoji.

 

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

“Kowa ya yi gwagwarmaya sosai a tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda kafafen yaɗa labarai ke kan gaba wajen yaƙi da mulkin kama-karya na soji.

 

“Saboda haka, shekaru 24 bayan haka, bai kamata a ga kafafen yaɗa labarai sun yi ƙasa a gwiwa ba a wannan muhimmin lokaci. Abin da ya kamata su yi shi ne ci gaba da ƙarfafa goyon bayansu ga dimokuraɗiyya.”

 

Ministan ya tabbatar wa shugabannin NGE, ƙarƙashin jagorancin Shugaban NGE, Eze Anaba, kan ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare martabar dimokraɗiyya, gami da ‘yancin yaɗa labarai.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai da su zama jagororin kare dimokuraɗiyyar Nijeriya, da inganta zaman lafiya, haɗin kai, da tsaron ƙasa wajen yaɗa lamuran ƙasa.

 

Idris ya ci gaba da bayyana cewa ajandar kawo sauyi na gwamnatin Tinubu na ci gaba da gudana, ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su bayyana abubuwa masu kyau, yana mai cewa Nijeriya na kan hanyar zuwa wani sabon zamani na ci gaban zamantakewa da tattalin arziƙi, wanda ke zuwa da ƙalubale.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren yaɗa labarai ta hanyar ayyuka na musamman kamar bayar da lamuni ta Bankin Masana’antu da magance tsadar buga jaridu.

 

A nasa jawabin, Anaba ya bayyana muhimmancin taron ANEC da ke tafe a Jihar Bayelsa, inda ya bayyana cewa takensa, “Haɓaka Tattalin Arziƙi da Dabarun Ci Gaba a Ƙasa Mai Ɗimbin Albarkatu,” ya yi daidai da buƙatun da Nijeriya ke da shi a halin yanzu da kuma buƙatar neman mafita don samar da ci gaba.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
Next Post
Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.