ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga kafafen yaɗa labaran Nijeriya da kada su yi ƙasa a gwiwa wajen kare dimokuraɗiyyar ƙasar da aka kwashe shekaru 24 ana yi.

 

Ministan ya jaddada hakan ne a wata ziyarar ban girma da Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) ta kai masa a ofishinsa domin tattaunawa kan shirye-shiryen Babban Taron Editocin Nijeriya (ANEC) karo na 20, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 6-9 ga Nuwamba, 2024, a Yenagoa, Jihar Bayelsa.

ADVERTISEMENT
  • Dauke Lantarkin Arewa
  • Tawagar Likitocin Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Aikin Jinya Ga Asibitin Tanzaniya

Idris ya jaddada muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen tallafawa tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda ya tuna da muhimmiyar rawar da suka taka a gwagwarmaya da mulkin kama-karya na sojoji.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

“Kowa ya yi gwagwarmaya sosai a tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya, inda kafafen yaɗa labarai ke kan gaba wajen yaƙi da mulkin kama-karya na soji.

 

“Saboda haka, shekaru 24 bayan haka, bai kamata a ga kafafen yaɗa labarai sun yi ƙasa a gwiwa ba a wannan muhimmin lokaci. Abin da ya kamata su yi shi ne ci gaba da ƙarfafa goyon bayansu ga dimokuraɗiyya.”

 

Ministan ya tabbatar wa shugabannin NGE, ƙarƙashin jagorancin Shugaban NGE, Eze Anaba, kan ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare martabar dimokraɗiyya, gami da ‘yancin yaɗa labarai.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai da su zama jagororin kare dimokuraɗiyyar Nijeriya, da inganta zaman lafiya, haɗin kai, da tsaron ƙasa wajen yaɗa lamuran ƙasa.

 

Idris ya ci gaba da bayyana cewa ajandar kawo sauyi na gwamnatin Tinubu na ci gaba da gudana, ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su bayyana abubuwa masu kyau, yana mai cewa Nijeriya na kan hanyar zuwa wani sabon zamani na ci gaban zamantakewa da tattalin arziƙi, wanda ke zuwa da ƙalubale.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren yaɗa labarai ta hanyar ayyuka na musamman kamar bayar da lamuni ta Bankin Masana’antu da magance tsadar buga jaridu.

 

A nasa jawabin, Anaba ya bayyana muhimmancin taron ANEC da ke tafe a Jihar Bayelsa, inda ya bayyana cewa takensa, “Haɓaka Tattalin Arziƙi da Dabarun Ci Gaba a Ƙasa Mai Ɗimbin Albarkatu,” ya yi daidai da buƙatun da Nijeriya ke da shi a halin yanzu da kuma buƙatar neman mafita don samar da ci gaba.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.