• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi

by Umar Faruk and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu ababen hawa a Koko Besse, Jega da Birnin Kebbi sun yaba wa Sanata Muhammadu Adamu Aliero mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya kan gyaran gadar da ta ruguje da ta hada Arewa maso Yamma da Kudancin kasar nan.

 

Idan dai za a iya tunawa, gadar da ke tsakanin garuruwan Kuchi da Rara a kan babbar hanyar da ta hada jihohin Kebbi, Sokoto, da Neja ta rushe a ranar 29 ga watan Agusta.

  • ’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu
  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai

Ta ruguje ne a daren Lahadi sakamakon mamakon ruwan sama da ya addabi jihar Kebbi da sauran jihohin da ke makwabtaka da jihar kamar Sokoto, Zamfara da Neja.

 

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Sanata Aliero wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin sufurin kasa, ya gyara gadar da ta ruguje, wadda ta janyo wa masu ababen hawa da manoma da ke tuka titin wahala matuka bayan rugujewar ta.

 

Masu ababen hawa da manoman sun bayyana jin dadinsu tare da yabawa a hirarsu manema Labarai daban-daban a karamar hukumar Koko/Besse da Jega da Birnin kebbi.

 

Alhaji Yahaya Malami, direban ‘yan kasuwa, ya yabawa Sanata Aliero kan gyaran gadar da aka yi, ya ce kamar an maido da gadar kamar yadda take.

 

“Kafin gyaran gadar, mun fuskanci kalubale na tafiyar kan hanyar zuwa Kudancin kasar nan.

 

“Duk direban da zai je yankin Kudancin kasar nan sai ya bi Jega, sannan ya zarce zuwa kananan hukumomin Kalgo, Bunza, Suru, da Bagudo sannan ya koma hanyarsa ta yau da kullun a Koko-Basse don ci gaba da tafiya Kudancin kasar nan.

 

“Sakamakon tashin farashin man fetur, masu ababen hawa da fasinjoji sun fuskanci wahalhalu da yawa kafin su je yankin Kudancin kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kuma bukaci direbobin da su kara kaimi ga kokarin sanata da gwamnati na hana afkuwar hadurran mota ta hanyar samar da ingantattun hanyoyi ta hanyar gujewa wuce gona da iri da kuma cunkoso yayin tukun motocinsu a kan hanya.

 

“Gyaran gadar ya sauƙaƙa wahalhalun da muke fuskanta a cikin zirga-zirgar ababen hawa daga jihar Kebbi zuwa Yauri har zuwa Kudancin ƙasar nan.

 

“Mun yi tunanin cewa gadar da ta ruguje za ta dauki lokaci mai tsawo kafin a gyara ta, kuma yanzu an gyara ta.

 

“Mun yi farin ciki, kuma muna godiya ga Gwamnatin Tarayya da kuma Sanata Adamu Aleiro don ceton rayukanmu da na fasinjojinmu,” in ji shi.

 

Shi ma Malam Nura Abubakar ya bukaci masu ababen hawa da ke amfani da hanyar da su rika tuka mota cikin aminci da bin ka’idojin kiyaye hanya domin kare rayuka da dukiyoyi da ababen more rayuwa a yankin a yayin tafiya kan wannan babbar hanyar.

 

A nasa bangaren, Alhaji Tsoho Alaye-Jega, Magoya bayan Sanata Aleiro, ya yabawa Sanatan tare da yin kira ga jama’a da su yaba da kokarin Sanatan na samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummarsa a jihar.

 

“Wannan gadar hanyar gwamnatin tarayya ce, amma Sanata Muhammadu Adamu Aleiro ya dauki nauyin gyara ta saboda muhimmancinta na tattalin arziki ga jama’ar wanda ba na jihar Kebbi kadai ba, har ma daga jahohin Sakkwato, Zamfara da Neja da sauransu.

 

“Dole ne mu gode masa kan abin da ya yi a yanzu, da abin da yake yi wa mutanen jihar Kebbi.

 

“Wannan ya nuna cewa muna da wakili nagari mai wakiltar mazabarmu na Kebbi ta tsakiya, kuma muna kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi da shi,” inji shi.

 

Alhaji Alaye-Jega, ya yi kira ga dukkan magoya bayan Sanata Aliero na gundumar Kebbi ta tsakiya da kuma sauran masu biyayya a fadin jihar da su ci gaba da marawa Sanatan baya don ganin an samar da karin gajiyar dimokradiyya daga hannun Sanatan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan More rayuwaKatsewar GadaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

6 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

7 hours ago
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

10 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

12 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

14 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

17 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.