• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi

by Umar Faruk and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu ababen hawa a Koko Besse, Jega da Birnin Kebbi sun yaba wa Sanata Muhammadu Adamu Aliero mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya kan gyaran gadar da ta ruguje da ta hada Arewa maso Yamma da Kudancin kasar nan.

 

Idan dai za a iya tunawa, gadar da ke tsakanin garuruwan Kuchi da Rara a kan babbar hanyar da ta hada jihohin Kebbi, Sokoto, da Neja ta rushe a ranar 29 ga watan Agusta.

  • ’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu
  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai

Ta ruguje ne a daren Lahadi sakamakon mamakon ruwan sama da ya addabi jihar Kebbi da sauran jihohin da ke makwabtaka da jihar kamar Sokoto, Zamfara da Neja.

 

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Sanata Aliero wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin sufurin kasa, ya gyara gadar da ta ruguje, wadda ta janyo wa masu ababen hawa da manoma da ke tuka titin wahala matuka bayan rugujewar ta.

 

Masu ababen hawa da manoman sun bayyana jin dadinsu tare da yabawa a hirarsu manema Labarai daban-daban a karamar hukumar Koko/Besse da Jega da Birnin kebbi.

 

Alhaji Yahaya Malami, direban ‘yan kasuwa, ya yabawa Sanata Aliero kan gyaran gadar da aka yi, ya ce kamar an maido da gadar kamar yadda take.

 

“Kafin gyaran gadar, mun fuskanci kalubale na tafiyar kan hanyar zuwa Kudancin kasar nan.

 

“Duk direban da zai je yankin Kudancin kasar nan sai ya bi Jega, sannan ya zarce zuwa kananan hukumomin Kalgo, Bunza, Suru, da Bagudo sannan ya koma hanyarsa ta yau da kullun a Koko-Basse don ci gaba da tafiya Kudancin kasar nan.

 

“Sakamakon tashin farashin man fetur, masu ababen hawa da fasinjoji sun fuskanci wahalhalu da yawa kafin su je yankin Kudancin kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kuma bukaci direbobin da su kara kaimi ga kokarin sanata da gwamnati na hana afkuwar hadurran mota ta hanyar samar da ingantattun hanyoyi ta hanyar gujewa wuce gona da iri da kuma cunkoso yayin tukun motocinsu a kan hanya.

 

“Gyaran gadar ya sauƙaƙa wahalhalun da muke fuskanta a cikin zirga-zirgar ababen hawa daga jihar Kebbi zuwa Yauri har zuwa Kudancin ƙasar nan.

 

“Mun yi tunanin cewa gadar da ta ruguje za ta dauki lokaci mai tsawo kafin a gyara ta, kuma yanzu an gyara ta.

 

“Mun yi farin ciki, kuma muna godiya ga Gwamnatin Tarayya da kuma Sanata Adamu Aleiro don ceton rayukanmu da na fasinjojinmu,” in ji shi.

 

Shi ma Malam Nura Abubakar ya bukaci masu ababen hawa da ke amfani da hanyar da su rika tuka mota cikin aminci da bin ka’idojin kiyaye hanya domin kare rayuka da dukiyoyi da ababen more rayuwa a yankin a yayin tafiya kan wannan babbar hanyar.

 

A nasa bangaren, Alhaji Tsoho Alaye-Jega, Magoya bayan Sanata Aleiro, ya yabawa Sanatan tare da yin kira ga jama’a da su yaba da kokarin Sanatan na samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummarsa a jihar.

 

“Wannan gadar hanyar gwamnatin tarayya ce, amma Sanata Muhammadu Adamu Aleiro ya dauki nauyin gyara ta saboda muhimmancinta na tattalin arziki ga jama’ar wanda ba na jihar Kebbi kadai ba, har ma daga jahohin Sakkwato, Zamfara da Neja da sauransu.

 

“Dole ne mu gode masa kan abin da ya yi a yanzu, da abin da yake yi wa mutanen jihar Kebbi.

 

“Wannan ya nuna cewa muna da wakili nagari mai wakiltar mazabarmu na Kebbi ta tsakiya, kuma muna kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi da shi,” inji shi.

 

Alhaji Alaye-Jega, ya yi kira ga dukkan magoya bayan Sanata Aliero na gundumar Kebbi ta tsakiya da kuma sauran masu biyayya a fadin jihar da su ci gaba da marawa Sanatan baya don ganin an samar da karin gajiyar dimokradiyya daga hannun Sanatan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan More rayuwaKatsewar GadaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

4 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

8 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.