• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Ababen More Rayuwa: Bankin Keystone Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara 

by Sulaiman and Hussein Yero
6 months ago
in Labarai
0
Samar Da Ababen More Rayuwa: Bankin Keystone Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin Keystone ya jinjina wa namijin ƙoƙarin Gwamna Lawal wajen samar da manyan abubuwan more rayuwa ga al’ummar Jihar Zamfara.

 

Manajan Daraktan Bankin, Hassan Imam ne ya jagoranci manyan jami’an gudanarwar bankin a ziyarar ban girma da suka kai wa gwamnan, ranar Asabar a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Tinubu Ya Isa Kasar Saudiyya Domin Taron Hadin Kan Kasashen Larabawa Da Musulunci
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa bankin na gyaran makarantar firamare ta Sarkin Kudu da kuma makarantar sakandare ta Sambo, duk a babban birnin jihar, a matsayin wani ɓangare na kyautata wa al’ummar da ake kira ‘Corporate Social Responsibility’ (CSR).

Yayin da yake jawabi ga shugabannin bankin, Gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin Keystone tare da jajircewarsu wajen ganin jihar Zamfara ta kasance cikin yanayi mai kyau ga kowane ɗan kasuwa.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

“Sanin kowa ne cewa mun gaji tsarin da ba ya aiki sosai a jihar Zamfara. Duk da haka, wannan ba uzuri ba ne na kasa yin aiki yadda ya kamata. A maimakon haka, mun mai da hankali kan lalubo mafi kyawun hanyoyin ci gaban jihar, kuma abin da muka tsayu a kai kenan.

“Ilimi yana da matuƙar muhimmanci ga duk abin da muke yi a rayuwar mu. Ya zama ƙashin bayan kowace ingantacciyar al’umma. A gwamnatina ilimi shi ne abu na biyu bayan tsaro.

“Ina so in nuna godiyata da wannan karimcin. Kamar yadda na ambata, wannan aiki zai shiga cikin tarihi a matsayin shaida ga rawar da bankin ku ke takawa a tarihin nasararmu.

“In Sha Allahu, Zamfara za ta ƙara ƙaimi da jajirce wajen ganin mun yi gogayya da sauran jihohin Nijeriya ta kowane fanni.

Zamfara

“Ina fatan ƙaddamar da waɗannan makarantu nan ba da jimawa ba da kammala su. Na gode ƙwarai da wannan karamci.

Tun da farko, Manajan Daraktan Bankin Keystone, Hassan Imam, ya bayyana cewa, hukumar gudanarwar bankin ta tattauna ne kan batun shiga tsakani kafin yanke shawarar mayar da hankali kan sake gyarawa da kuma inganta makarantu gaba ɗaya a wani bangare na Kyautata Wa Al’umma.

“Nasarar da wannan gwamnati ta samu a cikin watanni 17 kacal ya zarce abin da magabatanta suka cimma a cikin sama da shekaru 20. Gwamnatin Dauda ta yi fice a fannin ilimi, lafiya, da ababen more rayuwa. Bani da isasshen lokacin da zan jera duk abin da ta yi wa jihar Zamfara, amma duk wanda ya ziyarci jihar zai shaida yadda aka yi aikin titi na biliyoyin daloli.

“Mun zo nan ne domin mu ba ku goyon baya, saboda mun fahimci kwazon da ku ke yi, bayan tattaunawa da dama, mun yanke shawarar mayar da hankali kan ilimi, sannan muka zabi makarantun firamare da sakandare guda biyu. Muna gudanar da cikakken gyare-gyare a Makarantar Firamare ta Sarkin Kudu da Makarantar Sakandare ta Sambo, da ke babban birnin jihar.

“A halin yanzu ‘yan kwangilar sun riga sun isa wurin, kuma aiki ya kankama,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Isa Kasar Saudiyya Domin Taron Hadin Kan Kasashen Larabawa Da Musulunci

Next Post

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 70 A Borno

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

8 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

11 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

13 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

16 hours ago
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Fiye Da 70 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.