ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Ababen More Rayuwa: Bankin Keystone Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara 

by Sulaiman and Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Bankin Keystone ya jinjina wa namijin ƙoƙarin Gwamna Lawal wajen samar da manyan abubuwan more rayuwa ga al’ummar Jihar Zamfara.

 

Manajan Daraktan Bankin, Hassan Imam ne ya jagoranci manyan jami’an gudanarwar bankin a ziyarar ban girma da suka kai wa gwamnan, ranar Asabar a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Isa Kasar Saudiyya Domin Taron Hadin Kan Kasashen Larabawa Da Musulunci
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa bankin na gyaran makarantar firamare ta Sarkin Kudu da kuma makarantar sakandare ta Sambo, duk a babban birnin jihar, a matsayin wani ɓangare na kyautata wa al’ummar da ake kira ‘Corporate Social Responsibility’ (CSR).

Yayin da yake jawabi ga shugabannin bankin, Gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin Keystone tare da jajircewarsu wajen ganin jihar Zamfara ta kasance cikin yanayi mai kyau ga kowane ɗan kasuwa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Sanin kowa ne cewa mun gaji tsarin da ba ya aiki sosai a jihar Zamfara. Duk da haka, wannan ba uzuri ba ne na kasa yin aiki yadda ya kamata. A maimakon haka, mun mai da hankali kan lalubo mafi kyawun hanyoyin ci gaban jihar, kuma abin da muka tsayu a kai kenan.

“Ilimi yana da matuƙar muhimmanci ga duk abin da muke yi a rayuwar mu. Ya zama ƙashin bayan kowace ingantacciyar al’umma. A gwamnatina ilimi shi ne abu na biyu bayan tsaro.

“Ina so in nuna godiyata da wannan karimcin. Kamar yadda na ambata, wannan aiki zai shiga cikin tarihi a matsayin shaida ga rawar da bankin ku ke takawa a tarihin nasararmu.

“In Sha Allahu, Zamfara za ta ƙara ƙaimi da jajirce wajen ganin mun yi gogayya da sauran jihohin Nijeriya ta kowane fanni.

Zamfara

“Ina fatan ƙaddamar da waɗannan makarantu nan ba da jimawa ba da kammala su. Na gode ƙwarai da wannan karamci.

Tun da farko, Manajan Daraktan Bankin Keystone, Hassan Imam, ya bayyana cewa, hukumar gudanarwar bankin ta tattauna ne kan batun shiga tsakani kafin yanke shawarar mayar da hankali kan sake gyarawa da kuma inganta makarantu gaba ɗaya a wani bangare na Kyautata Wa Al’umma.

“Nasarar da wannan gwamnati ta samu a cikin watanni 17 kacal ya zarce abin da magabatanta suka cimma a cikin sama da shekaru 20. Gwamnatin Dauda ta yi fice a fannin ilimi, lafiya, da ababen more rayuwa. Bani da isasshen lokacin da zan jera duk abin da ta yi wa jihar Zamfara, amma duk wanda ya ziyarci jihar zai shaida yadda aka yi aikin titi na biliyoyin daloli.

“Mun zo nan ne domin mu ba ku goyon baya, saboda mun fahimci kwazon da ku ke yi, bayan tattaunawa da dama, mun yanke shawarar mayar da hankali kan ilimi, sannan muka zabi makarantun firamare da sakandare guda biyu. Muna gudanar da cikakken gyare-gyare a Makarantar Firamare ta Sarkin Kudu da Makarantar Sakandare ta Sambo, da ke babban birnin jihar.

“A halin yanzu ‘yan kwangilar sun riga sun isa wurin, kuma aiki ya kankama,” in ji shi.

Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Zamfara
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Fiye Da 70 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.