ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Ababen More Rayuwa: Bankin Keystone Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara 

by Sulaiman and Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Bankin Keystone ya jinjina wa namijin ƙoƙarin Gwamna Lawal wajen samar da manyan abubuwan more rayuwa ga al’ummar Jihar Zamfara.

 

Manajan Daraktan Bankin, Hassan Imam ne ya jagoranci manyan jami’an gudanarwar bankin a ziyarar ban girma da suka kai wa gwamnan, ranar Asabar a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Isa Kasar Saudiyya Domin Taron Hadin Kan Kasashen Larabawa Da Musulunci
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa bankin na gyaran makarantar firamare ta Sarkin Kudu da kuma makarantar sakandare ta Sambo, duk a babban birnin jihar, a matsayin wani ɓangare na kyautata wa al’ummar da ake kira ‘Corporate Social Responsibility’ (CSR).

Yayin da yake jawabi ga shugabannin bankin, Gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin Keystone tare da jajircewarsu wajen ganin jihar Zamfara ta kasance cikin yanayi mai kyau ga kowane ɗan kasuwa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Sanin kowa ne cewa mun gaji tsarin da ba ya aiki sosai a jihar Zamfara. Duk da haka, wannan ba uzuri ba ne na kasa yin aiki yadda ya kamata. A maimakon haka, mun mai da hankali kan lalubo mafi kyawun hanyoyin ci gaban jihar, kuma abin da muka tsayu a kai kenan.

“Ilimi yana da matuƙar muhimmanci ga duk abin da muke yi a rayuwar mu. Ya zama ƙashin bayan kowace ingantacciyar al’umma. A gwamnatina ilimi shi ne abu na biyu bayan tsaro.

“Ina so in nuna godiyata da wannan karimcin. Kamar yadda na ambata, wannan aiki zai shiga cikin tarihi a matsayin shaida ga rawar da bankin ku ke takawa a tarihin nasararmu.

“In Sha Allahu, Zamfara za ta ƙara ƙaimi da jajirce wajen ganin mun yi gogayya da sauran jihohin Nijeriya ta kowane fanni.

Zamfara

“Ina fatan ƙaddamar da waɗannan makarantu nan ba da jimawa ba da kammala su. Na gode ƙwarai da wannan karamci.

Tun da farko, Manajan Daraktan Bankin Keystone, Hassan Imam, ya bayyana cewa, hukumar gudanarwar bankin ta tattauna ne kan batun shiga tsakani kafin yanke shawarar mayar da hankali kan sake gyarawa da kuma inganta makarantu gaba ɗaya a wani bangare na Kyautata Wa Al’umma.

“Nasarar da wannan gwamnati ta samu a cikin watanni 17 kacal ya zarce abin da magabatanta suka cimma a cikin sama da shekaru 20. Gwamnatin Dauda ta yi fice a fannin ilimi, lafiya, da ababen more rayuwa. Bani da isasshen lokacin da zan jera duk abin da ta yi wa jihar Zamfara, amma duk wanda ya ziyarci jihar zai shaida yadda aka yi aikin titi na biliyoyin daloli.

“Mun zo nan ne domin mu ba ku goyon baya, saboda mun fahimci kwazon da ku ke yi, bayan tattaunawa da dama, mun yanke shawarar mayar da hankali kan ilimi, sannan muka zabi makarantun firamare da sakandare guda biyu. Muna gudanar da cikakken gyare-gyare a Makarantar Firamare ta Sarkin Kudu da Makarantar Sakandare ta Sambo, da ke babban birnin jihar.

“A halin yanzu ‘yan kwangilar sun riga sun isa wurin, kuma aiki ya kankama,” in ji shi.

Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Zamfara
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Fiye Da 70 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.