ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Tarihi

A bana ne ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin duniya na kin mafarkin murdiya. Tarihi ya nuna mana cewa, tabbatar da adalci ya kasance alkiblar al’ummar dan Adam ta dindindin. Ko da yake a wani lokaci mugunta ta samu damar mai da hannun agogo baya, amma a karshe abubuwa za su koma daidai.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, lokacin da motocin yaki na Jamus suka murkushe kauyuka a kasashen gabashin Turai, kuma jiragen saman yaki na Japan suka jefa bama-bamai a kasar Sin da mai da biranenta zuwa kufai: da alama kasashen sun kasance masu karfi da ba za su taba shan kaye ba. Amma a karkashin turjiyar mutane masu adalci na duniya, ‘yan mulkin zalunci ba za su iya magance faduwar totuwa da fuskantar hukunci a karshe ba. Mugunta ba za ta iya lashe adalci ba, wannan yana cikin ka’idojin tarihi.

  • Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
  • Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Sai dai har yanzu, bil’adama suna ci gaba da fuskantar ayyukan dake neman mai da hannun agogo baya: tunanin mulkin danniya, da ra’ayi na daukar matakin kashin kai, da na kariyar ciniki, suna yaduwa a duniya. Wasu kasashe sun kaddamar da yakin cinikayya da na haraji, wadanda suka yi matukar illata tattalin arzikin duniya da kuma karya dokokin cinikayya na kasa da kasa. Amma masu kare adalci suna nan a ko da yaushe, wadanda ke kokarin mayar da duniya kan turba mai dacewa, kuma kasar Sin na daya daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

A gun taron kolin BRICS da aka gudanar jiya ta yanar gizo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda uku a cikin jawabinsa: Wato tsayawa kan manufar cudanyar sassa daban-daban, da kiyaye daidaito da adalci a duniya; da tabbatar da bude kofa da cin moriya tare, don kare tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa; da kuma tabbatar da hadin kai a kokarin samun ci gaba na bai daya. Wadannan shawarwari, sun kunshi kalmomi na nuna sassaucin ra’ayi, amma ma’anarsu na cike da adalci. Suna wakiltar martanin kasar Sin game da yunkurin mayar da hannun agogo baya da ake fuskanta a halin yanzu a fagen kasa da kasa, wadanda ke nuna yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da gaskiya da adalci, da neman hadin kai, da sa kaimi ga tabbatar da moriyar juna a duk fadin duniya. Wannan tsari na adalci shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin samun cikakken goyon baya daga mafi yawan kasashen duniya.

Tabbas, ya kamata a kiyaye adalci ta hanyar aikace-aikace maimakon magana. Mu dauki yakin haraji da Amurka ta kaddamar kan Afirka a misali: Bayan da Amurka ta sauya manufarta ta ciniki da kasashen Afirka, da sanya musu harajin fito mai yawa da ya kai kaso 15 zuwa kaso 30 cikin 100, nan da nan kasar Sin ta fara taimakawa kasashen Afirka, inda ta sanar da cewa, za ta yafe dukkan harajin da ake karba kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla hulda da ita, suka fitar zuwa cikin gidanta. Wannan matakin ya aike da wani sako mai kyau ga Afirka, wato kasar Sin na son raba damar samun ci gaba tare da kasashen Afirka, da hadin kai da su don tinkarar hadurra. Lamarin da ya samu yabo daga masana tattalin arziki na kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kana wasu alkaluman da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta fitar sun nuna cewa, a cikin watanni 7 na farkon wannan shekara, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashe mafi karancin ci gaba a nahiyar Afirka, wadanda Sin ta riga ta yafe musu dukkan haraji, ta kai dalar Amurka biliyan 39.66, adadin da ya karu da kaso 10.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin a bara. Ta hanyar karfafa hadin gwiwar cinikayya da abokan hulda kamar Sin, da inganta cinikayya a cikin nahiya, ana sa ran ganin Afirka za ta samu nasarar rage tasirin manufar harajin Amurka.

A halin yanzu, kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin da kasashen Afirka, suna kokarin daukaka ra’ayin cudanyar sassa daban daban, da na bude kofa, da yin hadin gwiwa tare da tabbatar da moriyar juna, da hadin kai da juna, a karkashin laimar tsare-tsaren hadin gwiwa irin na BRICS, kuma suna tafiya zuwa gaba kan wata turba mai adalci. Tabbas babu wani karfi da zai iya hana su cimma buri da samun nasara. (Bello Wang)

 

Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • Sulaiman
    An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.