ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Tarihi

A bana ne ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin duniya na kin mafarkin murdiya. Tarihi ya nuna mana cewa, tabbatar da adalci ya kasance alkiblar al’ummar dan Adam ta dindindin. Ko da yake a wani lokaci mugunta ta samu damar mai da hannun agogo baya, amma a karshe abubuwa za su koma daidai.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, lokacin da motocin yaki na Jamus suka murkushe kauyuka a kasashen gabashin Turai, kuma jiragen saman yaki na Japan suka jefa bama-bamai a kasar Sin da mai da biranenta zuwa kufai: da alama kasashen sun kasance masu karfi da ba za su taba shan kaye ba. Amma a karkashin turjiyar mutane masu adalci na duniya, ‘yan mulkin zalunci ba za su iya magance faduwar totuwa da fuskantar hukunci a karshe ba. Mugunta ba za ta iya lashe adalci ba, wannan yana cikin ka’idojin tarihi.

  • Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
  • Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Sai dai har yanzu, bil’adama suna ci gaba da fuskantar ayyukan dake neman mai da hannun agogo baya: tunanin mulkin danniya, da ra’ayi na daukar matakin kashin kai, da na kariyar ciniki, suna yaduwa a duniya. Wasu kasashe sun kaddamar da yakin cinikayya da na haraji, wadanda suka yi matukar illata tattalin arzikin duniya da kuma karya dokokin cinikayya na kasa da kasa. Amma masu kare adalci suna nan a ko da yaushe, wadanda ke kokarin mayar da duniya kan turba mai dacewa, kuma kasar Sin na daya daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

A gun taron kolin BRICS da aka gudanar jiya ta yanar gizo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda uku a cikin jawabinsa: Wato tsayawa kan manufar cudanyar sassa daban-daban, da kiyaye daidaito da adalci a duniya; da tabbatar da bude kofa da cin moriya tare, don kare tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa; da kuma tabbatar da hadin kai a kokarin samun ci gaba na bai daya. Wadannan shawarwari, sun kunshi kalmomi na nuna sassaucin ra’ayi, amma ma’anarsu na cike da adalci. Suna wakiltar martanin kasar Sin game da yunkurin mayar da hannun agogo baya da ake fuskanta a halin yanzu a fagen kasa da kasa, wadanda ke nuna yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da gaskiya da adalci, da neman hadin kai, da sa kaimi ga tabbatar da moriyar juna a duk fadin duniya. Wannan tsari na adalci shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin samun cikakken goyon baya daga mafi yawan kasashen duniya.

Tabbas, ya kamata a kiyaye adalci ta hanyar aikace-aikace maimakon magana. Mu dauki yakin haraji da Amurka ta kaddamar kan Afirka a misali: Bayan da Amurka ta sauya manufarta ta ciniki da kasashen Afirka, da sanya musu harajin fito mai yawa da ya kai kaso 15 zuwa kaso 30 cikin 100, nan da nan kasar Sin ta fara taimakawa kasashen Afirka, inda ta sanar da cewa, za ta yafe dukkan harajin da ake karba kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla hulda da ita, suka fitar zuwa cikin gidanta. Wannan matakin ya aike da wani sako mai kyau ga Afirka, wato kasar Sin na son raba damar samun ci gaba tare da kasashen Afirka, da hadin kai da su don tinkarar hadurra. Lamarin da ya samu yabo daga masana tattalin arziki na kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Kana wasu alkaluman da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta fitar sun nuna cewa, a cikin watanni 7 na farkon wannan shekara, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashe mafi karancin ci gaba a nahiyar Afirka, wadanda Sin ta riga ta yafe musu dukkan haraji, ta kai dalar Amurka biliyan 39.66, adadin da ya karu da kaso 10.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin a bara. Ta hanyar karfafa hadin gwiwar cinikayya da abokan hulda kamar Sin, da inganta cinikayya a cikin nahiya, ana sa ran ganin Afirka za ta samu nasarar rage tasirin manufar harajin Amurka.

A halin yanzu, kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin da kasashen Afirka, suna kokarin daukaka ra’ayin cudanyar sassa daban daban, da na bude kofa, da yin hadin gwiwa tare da tabbatar da moriyar juna, da hadin kai da juna, a karkashin laimar tsare-tsaren hadin gwiwa irin na BRICS, kuma suna tafiya zuwa gaba kan wata turba mai adalci. Tabbas babu wani karfi da zai iya hana su cimma buri da samun nasara. (Bello Wang)

 

Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Sulaiman
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

LABARAI MASU NASABA

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.