• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Zai Sanya Hannu Kan Takardar Kashe Malamin Nan Da Ya Kashe Daliba Hanifa — Gwamnatin Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
ganduje

Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano, M. A. Lawal, ya ce, babu wani abun da zai dakatar da gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga ciki alkawarin da ya dauka na rattaba hannu kan takardar kisa ga makashin karamar daliba ‘yar shekara biyar, Hanifa da zarar aka kammala cika ka’idojin da shari’a ta gindaya.

Kwamishinan wanda yake magana kan mataki na gaba da gwamnatin jihar zata dauka kan matsayar hukuncin da mai shari’a, Usman Na’aba, ya yanke, ya yi bayanin cewa mutum biyun da aka yanke wa hukuncin kisan su na da damar daukaka kara cikin wata uku zuwa kotun gaba da Kotun da ta yanke musu hukunci.

“Kotu ta yanke wa mutum biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya, don haka gwamna ya yi alkawarin sanya hannu kan hukuncin kisa, don haka muna jiran kwanaki 90 su cika na damar daukaka kara kafin aiwatar da hakan,” Cewar Kwamishina.

Kwamishinan ya tabbatar da cewa alkawarin da suka yi tabbas a shirye suke su aiwatar amma dole su bi ka’idoji da matakan da shari’a ta ware wajen aiwatar da hakan.

Idan za ku iya tunawa dai Mai Shari’a Na’aba na babban kotun jihar Kano a makon jiya ya zartar da hukunci kan Tanko Abdulmalik, wanda ake zargi da kashe Hanifa, wanda kotun ta kama su dumu-dumu da laifin yin garkuwa da kashe karamar Dalian ‘yar shekara biyar a Kano wato Hanifa.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

Inda kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar ratayewa har sai sun mutu.

Sannan kuma kotun ta yanke wa Abddulmalik da abokin aikata laifin nasa hukuncin shekara biyar a gidan kurkuku bisa sauran laifuka uku da ta samesu da aikatawa daga cikin tuhume-tuhumen da ake musu.

Kazalika, wacce ake zargi ta uku, Fatima Musa, kuma an yanke mata hukuncin shekara biyu a gidan gyara halinka bisa samunta da aikata babban laifi da kokarin yin garkuwa.

Antoni Janar din ya kara da cewa, “A cikin wata shida, Alkali ya kammala shari’ar. Wannan abun jinjina ne. Idan suka daukaka kara za mu sanar da jama’a cewa a shirye muke da hakan a kowani lokaci.

“Ga mutanen da suke ta jefa ayar tambaya kan ko shin za a aiwatar da hukuncin ko a’a, duk abun da zan ce shi ne doka dai doka ce kuma zamu jira kwanaki 90 din da suke da damar daukaka kara su yi.

Idan sun daukaka kara, shi kenan, nan da nan za mu dauki matakin hakan, idan kuma ba su daukaka kara ba har lokacin ya wuce gwamnati za ta aiwatar da abun da ya dace.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Next Post
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.