• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa ta’azzarar matsalar tsaro a ‘yan kwanakin nan musamman a Babban Birnin Tarayya Abuja, dakarun Nijeriya sun yi sabon yunkuri domin murkushe barazanar da ake fuskanta musamman a cikin birnin da garuruwan da ke kewaye.

Majiyoyi daga rundunar soji sun shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, tun bayan harin da ‘yan bindiga suka kai wa Dogarawan Shugaban kasa ta ‘Guards Brigade’ kwanakin baya ya sanya rundunar sojin fadada ayyukansu na tsaro zuwa jihohin Neja, Nasarawa da Kogi domin kare babban birnin tarayyar daga hareharen ‘yan ta’adda.

Majiyar da ta nemi a sakaya sunanta, ta cigaba da cewa, sojojin suna kan farmakar ‘yan ta’adda a sansanonin da suka boye suna kai wa sojoji hare-hare da muhallan gwamnati.

Ta ba da tabbacin cewa dabarun da jami’an tsaro ke amfani da su a yanzu tabbas za su haifar da da mai ido domin kuwa sojoji suna samun nasarori sosai a kan ‘yan ta’addan tare da lalata musu shirye-shiryensu tun daga can maboyarsu, inda zuwa yanzu an kashe ‘yan ta’adda da dama kuma an kamo wasu.

Wakilinmu ya nakalto cewa an shiga zullumi a yankin Abuja a kan matsalar tsaro bayan wasu jerin manyan hare-hare guda uku na ‘yan ta’adda da suka auku.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Na farko shi ne kai hari gidan yarin Kuje wanda hakan ya kai ga tserewar fursunoni daban-daban ciki har da manyan ‘yan ta’adda 63 na kungiyar Boko Haram. Sai kuma harin da aka kai wa dogarawan shugaban kasa a Bwari inda maharan suka kashe wasu sojoji.

Bayan nan sun kuma kai hari ga shingen binciken sojoji da ke ‘Zuma Rock’ a kan iyakar Abuja da Jihar Neja wanda ya janyo jikkatar wasu sojoji, wadannan hare-haren sun jefa mazauna Abuja cikin firgici.

‘Yan ta’addan a wani faifayin bidiyo da suka sake, sun yi barazanar yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da sace Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da wasu fitattun ‘yan siyasa.

Domin kawo karshen matsalolin na tsaro, a halin yanzu rundunar sojin saman Nijeriya ta fara amfani da jiragen yaki samfurin A-29 Super Tucano da gwamnatin tarayya ta sayo su tun a watan Disambar shekarar 2018 amma suka shigo Nijeriya a watan Agustan 2021.

Kwangilar samar da jiragen tsakanin Gwamnatin Nijeriya da ta kasar Amurka ta kai Dala miliyan 500 da zimmar taimaka wa rundunar sojin saman Nijeriya wajen kawo karshen matsalolin tsaro musamman ‘yan ta’addan Boko Haram.

Shekara guda kenan da yin jigilar jiragen amma wasu na ganin an takura wa gwamnatin kasar da ka da ta yi amfani da jiragen kan ‘yan ta’addan inda su kuma ‘yan Boko Haram da mayakan ISWAP da na Ansaru da kuma ‘yan bindiga ke ci gaba da tsula tsiyarsu na ayyukan ta’addanci.

Rashin amfani da jiragen a shiyyar arewa maso gabas, da kuma arewa maso yamma da arewa ta tsakiya da kuma a ‘yan kwanakin nan maida hankali a Birnin Tarayya Abuja ya bai wa ‘yan ta’addan damar ci gaba da kai hare-hare.

A lokacin da aka tuntubi darakta yada labarai na rundunar sojin sama (NAF), Air Cdre Edward Gabkwet, ya ce, yanzu haka sun fara amfani da jiragen yakin na Tucano amma dai bai ba da cikakken bayani kan hakan ba.

Ya ce, bayyana wuraren da jiragen ke aiki a yanzu ba zai taimake su ba, don haka dai ya tabbatar da cewa jiragen suna kan kokarinsu na dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Kazalika, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin ‘yan sanda, Sanata Bala Ibn Na’Allah, a ranar Lahadi ya jinjina wa rundunar soji bisa fara amfani da jiragen yakin Super Tucano tare da irin nasaroroin da ake samu sakamakon amfani da su a halin yanzu wajen yaki da matsalar tsaro a kasar nan.

Ya bukaci rundunar sojin saman da ta ci gaba da kara kaimi kan wannan kokarin nata domin ganin an kawo karshen matsalolin tsaro da suka zama ruwan dare a kasar nan.

Ya kuma ce, samar da kayan aikin da suka dace ga dakaru abu ne da ya kamata gwamnati ta kara maida hankali a kai domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sufeto Janar Ya kara Yawan ‘Yan Sanda A Abuja

Shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya, IGP Usman Baba, ya tura karin jami’an ‘yansanda a cikin birnin tarayya Abuja domin tabbatar da kare mazauna birnin daga barazanar tsaro da ke addabar su a ‘yan kwanakin nan, tare da basu tabbacin cewa jami’an za su ci gaba da kokarin kare rayuka da dukiyar jama’an birnin.

Shugaban na ‘yansanda ya kuma umarci mataimakinsa mai kula da sashin ayyuka, DIG Bala Zama Senchi, da ya tabbatar da sanya ido a kan jami’an da aka tura domin tabbatar da suna ba da cikakkiyar kariya a yankin Abuja tare da jihohin da ke makwaftaka da ita.

Kazalika ya gargadi mazauna birnin dangane da yada labarun kanzun kurege da ka iya kara rurata matsaloli a maimakon taimaka wa jami’an tsaro.

Kakakin rundunar ‘yan sanda na kasa, CSP Olumuyiwa Adejobi ya kara da cewa, shugaban ‘yan sandan ya kuma bai wa ‘yan Nijeriya da mazauna Abuja tabbacin cewa za su ci gaba da kokarin kare rayukansu da dukiyarsu tare da dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Sannan, ya kara da neman hadin kan ‘yan Nijeriya da samar wa ‘yan sanda bayanan sirri domin taimaka musu wajen kawar da batagari a cikin kasar nan.

Shugaba Buhari Ya Roki Tallafin kasashen Waje Kan Matsalar Tsaro

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yaba wa kasashen waje bisa yadda suke tunkarar matsalolin tsaro da ke addabar duniya ciki kuwa har da Nijeriya.

Ya bukaci a kara samar da karin hadin guiwa a tsakani kasashe domin kawar da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro.

Da yake amsar wasika daga hannun babban wakilin kasar Kanada a Nijeriya, Ambasada James Kingston Christoff da Jakadan kasar Medico a Nijeriya, Juan Alfred Miranda Oritz, Shugaba Buhari ya fada wa jakadun cewa, an samu cimma muhimman nasarori ta hanyar yin aikin hadin guiwa tsakanin kasashe musamman a kan iyakoki, don haka akwai bukatar a kara azama a wannan fannin domin cimma nasarori masu tarin yawa.

Kakakin shugaban kasan, Mista Femi Adesina, a wata sanarwar da ya fitar shekaran jiya ya kara da cewa, “Duniya tana fama da matsalar tsaro da kuma na dumamar yanayi da kuma fama da aka yi da annobar Korona da suka janyo nakasu ga tattalin arzikin duniya, kasashe na ta yunkurin farfadowa daga wadannan matsalolin.

“Fadar da ke ci gaba da faruwa tsakanin kasashen Russia da Ukraine
ta haifar da nakasun wajen daidaito da matsalolin kasahe ke fuskanta, yayin da matsalar tsaro da ke faruwa a Libya ya kara janyo matsalar tsaro a yankunan Sahel tare da janyo nakasu ga dorewar demokradiyya a kasashen Afrika ta tsakiya da ta yamma.

“Nijeriya ma ba a barta a baya ba, muna ta fama da yaki da ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, rikicin manoma da makiyaya, da matsalar ‘yan ta’adda. Muna cimma nasarori ta hanyar hadin guiwa na kawance da kasashe irin naku na tabbata da gudunmawar da ake bayarwa za a kawo karshen wadannan matsalolin,” in ji shi.

Shugaba Buhari ya kara da cewa kasashen da suke karkashin kungiyar ECOWAS na hadin guiwa wajen magance matsalolin tsaro da rigingimun na kan iyakoki da sauran matsalolin da suke jibge kama daga na ‘yan ta’adda, safaran mutane ta barauniyar hanyoyi, safaran miyagun kwayoyi, garkuwa da mutane da sauransu.

“Na yi imani matsalar tsaro ya zama batun da ya shafi kowace kasa kuma a shirye kowace kasa take domin shawo kan hakan lamarin. Don haka
akwai bukatar kasashe su kara hadin guiwa da taimakon Nijeriya domin kawo karshen matsalolin tsaron nan da muke fama da su.”

Kazalika, Buhari ya yi amfani da wannan damar wajen neman kasashen wajen da su sanya ido kan zabukan da Nijeriya za ta gudanar a 2023 domin tabbatar da an yi zabuka masu cike da gaskiya da adalci kuma sahihi.

Daga bisani ya nemi Jakadun su dora a kan nasarorin da wadannan suka gada suka cimmar domin kyautata alakar kasashen.

Da ya ke jawabin godiya a madadin Jakadun, babban wakilin kasar Kanada, ya gode wa shugaba Buhari bisa amsar wasikar da suka kawo masa na jakadanci a Nijeriya.

Sun kuma ba shi tabbacin yin ayyukan hadaka domin cigaban kasashen.
Sannan, a shekaran jiya, Shugaba Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda harin ta’addanci na bayabayan nan ya shafa a jihohin Sokoto, Kaduna da Filato.
Shugaban ta cikin sanarwar da hadiminsa, Malam Garba Shehu ya fitar, ya bada tabbacin cewa gwamnatin tarayya za ta taimaki jihohin wajen shawo kan matsalolin da suke akwai, “Mun bai wa hukumomin tsaro cikakken ikon gudanar da aikin babu sani ko sabo kan ‘yan ta’addan. Na yi tir da hare-haren da ‘yan ta’adda ke kai wa a sassan kasar nan. Ina jajanta wa iyalan wadanda suka mutu tare da fatan Allah bai wa wadanda suka jikkata lafiya,” in ji shi.

‘Yan Ta’adda Sun Sako karin Wasu Fasinjojin Jirgin kasan Kaduna 5

Wasu karin mutum biyar daga cikin fasinjojin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga watan Maris sun shaki iskar ‘yanci a tsakiyar makon nan.

Wadanda aka sake din sun hada da Farfesa Mustapha Umar Imam, wanda Likita ne a asibitin koyarwa ta jami’ar Usman Dan Fodio (UDUS), Sakkwato.

Sauran kuma su ne Akibu Lawal, Abubakar Ahmed Rufai, Mukthar Shu’aibu Sidi and Aminu Sharif.

Mal Tukur Mamu, mawallafin jaridar ‘Desert Herald’ wanda ya taimaka wajen sulhu tsakanin gwamnati da masu garkuwa da mutanen ne ya tabbatar da sake mutum biyar din.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa fasinjojin jirgin kasan Kaduna su 63 ne aka yi garkuwa da su inda aka kashe mutum 9 daga cikinsu.

Ko a kwanakin baya ma dai masu garkuwan sun saki wani rukuni daga cikin wadanda suka yi garkuwa ciki har da manajan bankin noma tare da wasu mutum 11.

Inda zuwa yanzu aka saki mutum 24 daga cikin fasinjojin. Zuwa lokacin rubuta wannan rahoto dai Har yanzu dai zuwa yanzu sama da mutum 30 na hannun masu garkuwan.

Majalisa Ta Yi Ganawar Sirri Da Manyan Hafsoshi

A halin da ake ciki kuma Majalisar Dattawa ta yi wata ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaro da sauran shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri na tsaro bisa barazanar tsaron da ake fuskanta.

Shugaban majalisar, Sanata Ahmed Lawan ya jagoranci sauran shugabannin majalisar wajen gudanar da taron.

Yayin da shi kuma Babban Hafsan Hafsoshin Tsaro, Janar Lucky Irabo ya jagoranci shugabannin rundunonin tsaron zuwa taron.

A jawabinsa na bude taron kafin su shiga ganawar ta sirri, Sanata Ahmed Lawan ya bayyana cewa majalisar ta nuna dukufa sosai kamar takwararta sashen zartarwa wajen ware makudan kudi da amincewa da shi domin ganin an shawo kan matsalar tsaron da ta kawo wa kowa iya wuya, yana mai cewa shi ya sa suka kira taron don su fahimci a ina ne gizo yake sakar don warwarewa.

“Mun kira ku ne a yau domin abin da ya zama baro-baro a fili ga kowa, abin da yake gaban kowa a yanzu, abin da ya addabi kowane dan Nijeriya a yau.

Kafin majalisa mu tafi hutu a makon da ya gabata mun tattauna a kan yanayin tsaro a kasar nan, kuma kafin nan ma mun sha yi.

“Tun da aka dawo mulkin dimokuradiyya a kasar daga 1999 babu wata gwamnati da ta zuba makudan kudi a harkar tsaro kamar gwamnati mai ci… duk da mun san babu wata kasa da za ta ce tana da tsaro dari bisa dari amma akwai yanayin da in aka shiga babu wata kasar da hankalinta zai kwanta. A gaskiya yanayin namu ya tsawaita.

Mun sa ran cewa zuwa yanzu an samu saukin lamarin, kuma Nijeriya ta samu ci gaba ba kawai a sha’anin tsaron ba har da tattalin arziki.

Na yi ammanar rundunonin tsaro suna bakin kokarinsu amma a zahirin gaskiya ya kamata mu kara himma.” In ji shi.

Majalisar ta bayyana cewa daga yau (Laraba) tana so ta fara ganin sauyi a sha’anin tsaron kasar.

Da yake nasa jawabin, Janar Irabo ya gode wa majalisar bisa gayyatar su da ta yi domin tattauna matsalar, inda ya ce, “Na yi amannar cewa bisa hikimar da shugaban majalisa da sauran masu taimaka masa suke da ita ta tara wannan taro saboda yanayin tsaron kasa za a samu mafita. Domin duk yanayi ko halin da aka shiga akwai sararin da za a iya musanyar ra’ayoyi da fasahohi domin kowa ya bayar da gudunmawarsa a kai”.

Ya ce akwai abubuwa da dama da suka aiwatar kuma akwai karin wasu
da suka sa a gaba wanda ake sa ran su taimaka wajen samun nasara.

Daga bisani dai sun ci gaba da ganawarsu cikin sirri inda aka kulle wa ‘yan jarida kofa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujaBuhariJiragen YakiMatsalar TsaroYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Zai Sanya Hannu Kan Takardar Kashe Malamin Nan Da Ya Kashe Daliba Hanifa — Gwamnatin Kano

Next Post

Goron Juma’a

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

58 minutes ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

11 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

12 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

13 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

16 hours ago
Next Post
Goron Juma’a

Goron Juma’a

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.