ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Zai Sanya Hannu Kan Takardar Kashe Malamin Nan Da Ya Kashe Daliba Hanifa — Gwamnatin Kano

by Khalid Idris Doya
4 years ago
ganduje

Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano, M. A. Lawal, ya ce, babu wani abun da zai dakatar da gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga ciki alkawarin da ya dauka na rattaba hannu kan takardar kisa ga makashin karamar daliba ‘yar shekara biyar, Hanifa da zarar aka kammala cika ka’idojin da shari’a ta gindaya.

Kwamishinan wanda yake magana kan mataki na gaba da gwamnatin jihar zata dauka kan matsayar hukuncin da mai shari’a, Usman Na’aba, ya yanke, ya yi bayanin cewa mutum biyun da aka yanke wa hukuncin kisan su na da damar daukaka kara cikin wata uku zuwa kotun gaba da Kotun da ta yanke musu hukunci.

“Kotu ta yanke wa mutum biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya, don haka gwamna ya yi alkawarin sanya hannu kan hukuncin kisa, don haka muna jiran kwanaki 90 su cika na damar daukaka kara kafin aiwatar da hakan,” Cewar Kwamishina.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ya tabbatar da cewa alkawarin da suka yi tabbas a shirye suke su aiwatar amma dole su bi ka’idoji da matakan da shari’a ta ware wajen aiwatar da hakan.

Idan za ku iya tunawa dai Mai Shari’a Na’aba na babban kotun jihar Kano a makon jiya ya zartar da hukunci kan Tanko Abdulmalik, wanda ake zargi da kashe Hanifa, wanda kotun ta kama su dumu-dumu da laifin yin garkuwa da kashe karamar Dalian ‘yar shekara biyar a Kano wato Hanifa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Inda kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar ratayewa har sai sun mutu.

Sannan kuma kotun ta yanke wa Abddulmalik da abokin aikata laifin nasa hukuncin shekara biyar a gidan kurkuku bisa sauran laifuka uku da ta samesu da aikatawa daga cikin tuhume-tuhumen da ake musu.

Kazalika, wacce ake zargi ta uku, Fatima Musa, kuma an yanke mata hukuncin shekara biyu a gidan gyara halinka bisa samunta da aikata babban laifi da kokarin yin garkuwa.

Antoni Janar din ya kara da cewa, “A cikin wata shida, Alkali ya kammala shari’ar. Wannan abun jinjina ne. Idan suka daukaka kara za mu sanar da jama’a cewa a shirye muke da hakan a kowani lokaci.

“Ga mutanen da suke ta jefa ayar tambaya kan ko shin za a aiwatar da hukuncin ko a’a, duk abun da zan ce shi ne doka dai doka ce kuma zamu jira kwanaki 90 din da suke da damar daukaka kara su yi.

Idan sun daukaka kara, shi kenan, nan da nan za mu dauki matakin hakan, idan kuma ba su daukaka kara ba har lokacin ya wuce gwamnati za ta aiwatar da abun da ya dace.”

ganduje
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.