• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

byYusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
majalisar kasa

Kudirin zartaswa da ke gaban majalisun tarayya guda biyu na dokar sake fasalin haraji ya raba kan ‘yan majalisa daga yankin arewacin kasar nan.

 

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Ali Ndume a wata sanarwa da ya fitar a baya-bayan nan ya goyi bayan gwamnonin arewa da kungiyar tuntuba ta arewa (ACF), wadanda a tarurruka daban-daban suka yi watsi da kudirin dokar.

  • Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Ndume a cikin sanarwar ya yi nuni da cewa, manufofin tattalin arziki na gwamnati mai ci sun talautar da al’umma, sannan kuma ya yi ikirarin cewa sake fasalin harajin zai kara wa talakawan Nijeriya matsin tattalin arziki.

 

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ya ce, “Wannan harajin da suke magana a kai, mun kusan rasa masu matsakaicin karfi a Nijeriya. Ko kana da shi ko ba ka da shi. Wadanda suke a tsakiya ana matse su. Idan ’yan Nijeriya za su iya biyan wadannan haraji, ba komai.

 

“Amma a halin da ake ciki yanzu, kara haraji ba mafita ba. Ba zan goyi bayan wani karin haraji ba.”

 

Sai dai da yake magana a ranar Litinin a Abuja, dan rajin kare hakkin Bil’adama kuma tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya a majalisar wakilai ta 8, Shehu Sani, ya yi ikirarin cewa Sanata Ndume da wasu da ke kalubalantar shirin garambawul na harajin da ake shirin yi ba magana ce ta ilimi ba.

 

Ya ci gaba da cewa arewa kamar sauran sassan kasar nan za su ci gajiyar wannan sauyi na haraji.

 

Ya dage kan cewa kudirorin sake fasalin harajin ba su shafi arewa ba kamar yadda Ndume da makarrabansa ke bayyanawa, amma arewa ta tsaya kyam wajen yin kwaskwarimar da za ta sanya harajin VAT a hannun kowace jiha don sarrafa shi.

 

Sani ya ce wannan garambawul na iya haifar da sauyi daga tsarin haraji na baya da kuma sabon tsarin samar da kudaden shiga, domin zai magance matsalolin ‘yan kasuwa da za su iya yin duk wani abu don kaucewa kudaden haraji da kuma neman hana harajin da ba dole ba.

 

Ya yi gargadin cewa tattalin arzikin kasar zai yi matukar kaduwa idan aka soke kudirorin gyara haraji, inda ya yi Allah-wadai da kin amincewar da gwamnonin jihohin arewa suka yi na sake fasalin. Ya shawarci gwamnonin jihohin da su sa masu ba da shawara su yi nazari a kan kudirin, idan ba su da lokacin yin shi da kansu.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version