• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kudirin zartaswa da ke gaban majalisun tarayya guda biyu na dokar sake fasalin haraji ya raba kan ‘yan majalisa daga yankin arewacin kasar nan.

 

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Ali Ndume a wata sanarwa da ya fitar a baya-bayan nan ya goyi bayan gwamnonin arewa da kungiyar tuntuba ta arewa (ACF), wadanda a tarurruka daban-daban suka yi watsi da kudirin dokar.

  • Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Ndume a cikin sanarwar ya yi nuni da cewa, manufofin tattalin arziki na gwamnati mai ci sun talautar da al’umma, sannan kuma ya yi ikirarin cewa sake fasalin harajin zai kara wa talakawan Nijeriya matsin tattalin arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Ya ce, “Wannan harajin da suke magana a kai, mun kusan rasa masu matsakaicin karfi a Nijeriya. Ko kana da shi ko ba ka da shi. Wadanda suke a tsakiya ana matse su. Idan ’yan Nijeriya za su iya biyan wadannan haraji, ba komai.

 

“Amma a halin da ake ciki yanzu, kara haraji ba mafita ba. Ba zan goyi bayan wani karin haraji ba.”

 

Sai dai da yake magana a ranar Litinin a Abuja, dan rajin kare hakkin Bil’adama kuma tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya a majalisar wakilai ta 8, Shehu Sani, ya yi ikirarin cewa Sanata Ndume da wasu da ke kalubalantar shirin garambawul na harajin da ake shirin yi ba magana ce ta ilimi ba.

 

Ya ci gaba da cewa arewa kamar sauran sassan kasar nan za su ci gajiyar wannan sauyi na haraji.

 

Ya dage kan cewa kudirorin sake fasalin harajin ba su shafi arewa ba kamar yadda Ndume da makarrabansa ke bayyanawa, amma arewa ta tsaya kyam wajen yin kwaskwarimar da za ta sanya harajin VAT a hannun kowace jiha don sarrafa shi.

 

Sani ya ce wannan garambawul na iya haifar da sauyi daga tsarin haraji na baya da kuma sabon tsarin samar da kudaden shiga, domin zai magance matsalolin ‘yan kasuwa da za su iya yin duk wani abu don kaucewa kudaden haraji da kuma neman hana harajin da ba dole ba.

 

Ya yi gargadin cewa tattalin arzikin kasar zai yi matukar kaduwa idan aka soke kudirorin gyara haraji, inda ya yi Allah-wadai da kin amincewar da gwamnonin jihohin arewa suka yi na sake fasalin. Ya shawarci gwamnonin jihohin da su sa masu ba da shawara su yi nazari a kan kudirin, idan ba su da lokacin yin shi da kansu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mizanin Hajoji Da Hidimomi Da Masana’antun Kasar Sin Ke Samarwa Ya Karu Da Kaso 5.3 Bisa Dari A Watan Oktoba

Next Post

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

10 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

11 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
Haraji
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

16 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

17 hours ago
Next Post
An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.