ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
majalisar kasa

Kudirin zartaswa da ke gaban majalisun tarayya guda biyu na dokar sake fasalin haraji ya raba kan ‘yan majalisa daga yankin arewacin kasar nan.

 

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Ali Ndume a wata sanarwa da ya fitar a baya-bayan nan ya goyi bayan gwamnonin arewa da kungiyar tuntuba ta arewa (ACF), wadanda a tarurruka daban-daban suka yi watsi da kudirin dokar.

ADVERTISEMENT
  • Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Ndume a cikin sanarwar ya yi nuni da cewa, manufofin tattalin arziki na gwamnati mai ci sun talautar da al’umma, sannan kuma ya yi ikirarin cewa sake fasalin harajin zai kara wa talakawan Nijeriya matsin tattalin arziki.

 

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Ya ce, “Wannan harajin da suke magana a kai, mun kusan rasa masu matsakaicin karfi a Nijeriya. Ko kana da shi ko ba ka da shi. Wadanda suke a tsakiya ana matse su. Idan ’yan Nijeriya za su iya biyan wadannan haraji, ba komai.

 

“Amma a halin da ake ciki yanzu, kara haraji ba mafita ba. Ba zan goyi bayan wani karin haraji ba.”

 

Sai dai da yake magana a ranar Litinin a Abuja, dan rajin kare hakkin Bil’adama kuma tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya a majalisar wakilai ta 8, Shehu Sani, ya yi ikirarin cewa Sanata Ndume da wasu da ke kalubalantar shirin garambawul na harajin da ake shirin yi ba magana ce ta ilimi ba.

 

Ya ci gaba da cewa arewa kamar sauran sassan kasar nan za su ci gajiyar wannan sauyi na haraji.

 

Ya dage kan cewa kudirorin sake fasalin harajin ba su shafi arewa ba kamar yadda Ndume da makarrabansa ke bayyanawa, amma arewa ta tsaya kyam wajen yin kwaskwarimar da za ta sanya harajin VAT a hannun kowace jiha don sarrafa shi.

 

Sani ya ce wannan garambawul na iya haifar da sauyi daga tsarin haraji na baya da kuma sabon tsarin samar da kudaden shiga, domin zai magance matsalolin ‘yan kasuwa da za su iya yin duk wani abu don kaucewa kudaden haraji da kuma neman hana harajin da ba dole ba.

 

Ya yi gargadin cewa tattalin arzikin kasar zai yi matukar kaduwa idan aka soke kudirorin gyara haraji, inda ya yi Allah-wadai da kin amincewar da gwamnonin jihohin arewa suka yi na sake fasalin. Ya shawarci gwamnonin jihohin da su sa masu ba da shawara su yi nazari a kan kudirin, idan ba su da lokacin yin shi da kansu.

 

Haraji
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Haraji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

MASU ALAKA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.