ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

by Sani Anwar and Sulaiman
2 years ago
World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU), ta zargi Babban Bankin Duniya da kuma Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) da yin zagon kasa, don lalata tsarin ilimin al’umma a Nijeriya.

 

Kungiyar ta kuma koka a kan jinkirin da aka samu wajen sake tattaunawa da gwamnatin tarayya a shekarar 2009, inda ta ce duk da cewa, an cimma yarjejeniya da gwamnatin tarayyar da dama, amma har yanzu ba a kammala tattaunawar da kungiyar ta ASUU da kuma gwamnatin ba.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Kafa Tsarin Ilimin Koyar Da Sana’o’i Mafi Girma A Duniya
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA

Shuugaban na ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana hakan ranar Talata a Abuja; yayin bikin ranar jaruman kungiyar ta 2024 zuwa 2025.

 

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Har ila yau, shugaban ya yi nadamar bayyana yadda lamarin ya kara dagulewa sakamakon aiwatar da tsarin da aka cimma na IPPIS a jami’o’in gwamnati, bayan da majalisar zartarwa ta tarayya ta bayyana shirin cire tsarin daga makarantun gaba da sakandire.

 

Osodeke ya kuma nuna damuwarsa, kan yadda har yanzu gwamnatin tarayya ke ci gaba da rike wa kungiyar albashi na wata uku da rabi; ba bisa ka’ida ba, baya ga wasu bashisshikan albashin da na karin girma da kuma alawus-alawus, wanda har yanzu ba ta biya ba.

 

Da yake yin karin haske a wajen taron, inda kungiyar ASUU ta ta karrama wadanda ta bayyana a matsayin “Tsoffin jarumanta wadanda har yanzu ke raye”, Osodeke ya yaba wa ‘ya’yan kungiyar na kasa baki-daya, bisa “Jajircewa da sadaukar da kai da suka yi wajen wajen tabbatar da wannan kungiya tamu, wanda ke da nasaba da ‘yantar da al’ummar Nijeriya har abada.”

 

Har wa yau, ya kuma bayyana cewa; kungiyar za ta bayar da tallafin karo karatu na digirin-digirgir (Ph.D) ga wasu mambobinta a jami’o’in gwamnati daban-daban na wannan kasa. Tallafin, zai kasance na Naira 500,000 ga duk wanda ya yi katarin samu, sannan za a bayar da shi ne bisa la’akari da shawarwarin da kwararru daga cikin mambobin suka bayar.

 

“’Yan’uwa, kamar a baya ma; bikin na bana na jaruman namu na gudana ne a daidai lokacin da muke ci gaba da fafutukar ganin an ceto jami’o’in gwamnatin Nijeriya daga halin kunci, wanda Babban Bankin Duniya (World Bank) da Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) suka jefa su, wadanda yunkurinsu na ruguzawa ko binne tsarin jami’o’in bai yi nasara ba.

 

Wadanda aka karrama a wajen taron su ne; Farfesa T. Uzodinma Nwala; Farfesa Bright Ekuerhare; Farfesa Oye Oyediran; Mallam Bashir Kurfi; Farfesa The Name Ikiddeh; Mista S.A. Fadipe da kuma Farfesa Sola Olukunle.

 

Sauran sun hada da; Nasir Hussain; Tunde Oduleye; Farfesa Rasheed Abubakar; Akin Oyebode; Mustapha A. Danesi; A.T. Wins; and da kuma Peter Ozo-son.

Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.