• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kare Cin Bashi Duk Da Samun Ƙaruwar Kuɗaɗen Shiga

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Gwamnatin Tarayya Ta Kare Cin Bashi Duk Da Samun Ƙaruwar Kuɗaɗen Shiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta kare shirin ci bashin da ta ke yi, tana mai cewa an yi hakan ne bisa amincewar majalisar tarayya, duk da cewa hukumomin samar da kuɗaɗen shiga sun samu abinda suke hasashen samu na shekara.

Wannan bayani ya fito ne a taron tattaunawa tsakanin hukumomin samar da kuɗaɗen shiga da kwamitocin haɗin gwuiwa na majalisar tarayya kan kuɗi, da kasafin kuɗi, da tsare-tsaren tattalin arziki a Abuja.

  • Nijeriya Na Iya Samun Naira Tiriliyan 6.9 Na Kudin Shiga Daga Mai  A Wata Daya
  • Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti

A taron, hukumar Kwastam ta bayyana cewa ta tara Naira tiriliyan 5.352 har zuwa Satumba 2024, wuce Naira tiriliyan 5.09 na shekara da suke don samu. Haka kuma, NNPCL ta ce ta tara Naira tiriliyan 13.1, wuce kuɗin da suke burin samu na Naira tiriliyan 12.3 na 2024, yayin da FIRS ta bayyana cewa ta tara kuɗaɗen harajin da suke burin samu har da Naira tiriliyan 5.7 daga kamfanoni.

Duk da ƙaruwar kuɗaɗen shiga, ‘yan majalisa sun tambayi dalilin da yasa gwamnati ke ci gaba da neman rance a wajen Nijeriya?

Ministan kasafin kuɗi, Atiku Bagudu, ya bayyana cewa shirin cin bashi yana cikin kasafin kuɗin 2024 da aka tsara don magance gibin Naira tiriliyan 9.7. Ya ce, duk da ƙaruwar kuɗaɗen shiga, akwai buƙatar bashi domin cike gibin kasafi da tallafawa talakawa da marasa galihu.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Duk da haka, hukumar kula da shige da fice ta fuskanci suka kan yarjejeniyar PPP da ta bai wa kamfani 70% na kuɗin fasfo, inda aka umarce su da miƙa dukkan takardun yarjejeniyar domin duba wa nan da mako guda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Da Suka Ci Gaba Da Su Sauke Nauyi Na Ba Da Tallafin Kudin Sauyin Yanayi Ga Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Tabbatar Daidaiton Tsarin Masana’antu Da Na Samar Da Kayayyaki A Duniya

Related

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

58 minutes ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

3 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

4 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

12 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

13 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

13 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Tabbatar Daidaiton Tsarin Masana’antu Da Na Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Tabbatar Daidaiton Tsarin Masana'antu Da Na Samar Da Kayayyaki A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.