Matatar mai ta Fatakwal ta fara sarrafa danyen mai bayan jinkirin sanar da lokacin fara aiki har sau bakwai.
A baya matatar ta tsara fara aiki a watan Maris, sannan ta dage zuwa Agusta, da Satumban 2024.
- Gwamnatin Kebbi Ta Dakile Yunkurin Lakurawa Na Satar Shanu
- Mutum 1 Ya Rasu, An Ceto 14 Yayin Da ‘Yansanda Suka Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Katsina
Kamfanin Mai na Ƙasa (NNPCL) ne, ya bayyana wannan a matsayin babban ci gaba.
Kamfanin ya ce wannan zai zama mataki na kai wa ga dogaro da kai wajen samar da makamashi da bunkasa tattalin arziki.
An fara gyaran matatar a shekarar 2021 karkashin kamfanin Maire Tecnimont SpA, bayan sanya hannu kan kwangilar dala biliyan 1.5.
A watan Disamban 2023, aikin ya samu jinkiri saboda harkar da ta shafi tsaro da sauran matsaloli.
Fara aikin matatar zai zama babbar nasara ga Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp