• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi’u Ali

Ana Yi Wa 'Yan F im Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi'u Ali

by Rabilu Sanusi Bena
5 months ago
in Nishadi
0
Ana Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi’u Ali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jarumi kuma furodusa a masana’antar Kannywood wanda ya na daya daga cikin wadanda tauraruwarsu ta dade ta na haskawa a wannan masana’antar Ali Rabi’u Ali ya bayyana cewar ana yiwa masu yin wannan sana’a ta fim a matsayin malamai ko wasu masu gyaran tarbiyya a lokacin baya.

Ali Rabi’u wanda ya ce ya shafe fiye da shekara 25 da ya fara wannan harka a matsayin mai daukar hoto zuwa jarumi zuwa furodusa da kuma darakta, ya yi bayanai da dama a kan wannan masana’antar a wata hira da ya yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show inda ya tabbatar da cewar zimmar da yake da ita na koyar da wasu abubuwan da ya sani ne ya sa har ya fara shirya fina finai da kansa.

  • Bai Kamata Mutum Ya Dogara Da Harkar Fim Kadai Ba -Hamza Talle Mai Fata
  • Tun Kafin A Samu Masana’antar Kannywood Nake Harkar Fim – Lilisco

Tunda farko dai Ali ya yi bayani akan yadda yake daukar samuwar manhajar YouTube a cikin masana’antar Kannywood ba kamar yadda aka sani a baya ba, inda ya ce shekaru 10 da suka gabata ya taba wannan maganar inda ya tabbatar da cewar nan gaba za a koma dora fina-finai a yanar gizo da kuma kafafin talabijin na Satellite wanda kuma ya ce maganar da ya yi ga ta yanzu a zahiri domin kuwa komai ya koma yanar gizo ko kuma gidajen talabijin.

Sannan kuma ya ce zuwan soshiyal midiya yana da amfani amma kuma a wani bangaren ya matukar kasaara wannan harka ta fim, domin kuwa a yanzu yayin da ake cikin daukar sabon fim sai kaga wani ya zaro waya a aljihunsa ya na daukar bidiyon duk wani abu da ake yi a wajen lakeshin dinka na fim ya dora a shafinsa na Facebook ko Tik Tok.

Hakan da ya yi zai sa mutane su fara ganin fitowar da ka tsara a cikin shirinka tun kafin shirin ya shiga kasuwa,da haka ne zai sa masu kallo ba za su matsu fim dinka ya shiga kasuwa ba domin sun riga da sun ga wasu daga cikin abubuwan da fim din ya kunsa,ba kamar a lokacin baya da mutane za su kagu wajen jiran fim ya fito su kalla ba, saboda haka wannan hali da wasu daga cikin wadanda suke masana’antar suke yi ya matukar ragewa kasuwar fina-finai yawan ciniki.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Da yake amsa tambaya a kan minene matsayarsa dangane da wadanda ke yi wa jaruman fim kallon mutanen banza, Ali ya ce a tasa fahimtar babu wani mutum da zai lalace bayan shigowarshi wannan masana’anta ta Kannywood,domin kuwa duk idan kaga wani dan iska a Kannywood to dama can dan iska ne domin masana’antar Kannywood babu wanda ta taba mayarwa dan iska kowa da irin halinsa ya shigo cikinta inji shi.

Ya ci gaba da cewa a zamanin baya kafin yanzu mutane su na yi mana kallon wasu mutane da ke gyaran tarbiyya ta hanyar fina finansu ko kuma wasu malamai da ke isar da sako ta wata hanyar da ba wa’azi ba, saboda haka duk wanda kagani dan iska a masana’antar Kannywood dama can dan iska ne ba Kannywood ya koyi iskanci ba Ali ya tabbatar.

A kan yadda wasu daga cikin Kannywood ke kuka da abinda suke kira butulci da suke ganin wasu daga cikin wadanda suka yi renonsu a masana’antar domin ganin sun tsaya da kafafunsu kuma daga baya su juya masu baya, Ali ya ce ko kusa bai hadu da irin wannan ba domin kuwa dama bai taimaki wani a masana’antar Kannywood domin jiran wata rana ya rama mashi ba.

A duk lokacin da na taimaki wani a wannam harka ba na sa ran cewar wata rana zan nemi taimako a wajensa balle ya ki yi mani har raina ya baci in ji, ya ci gaba da cewa akwai da dama daga cikin wadanda tauraruwarsu ke haskawa a yanzu wanda ni na rene su tun kafin su san minene fim,a duk lokacin da na ji wani ya yabe su ko ya nuna sun burge shi har kuka nake yi domin kuwa nasan ta dalilina ne wannan mutumin ya kai wannan matsayi da ake ganinshi a yanzu.

Daga karshe Ali Rabi’u Ali ya bayyana cewar zuciyarsa ba ta mutu a jiran wani ya yi mashi ba,duk da cewar duk wani alheri da ake samu a wata sana’a ya sami kwatankwacin irin nashi a harkar fim amma ya na hadawa da kasuwanci a gefe kuma yanzu haka shi ma’aikacin gwamnati ne hakan ya sa yana da hanyoyin samun kudade da dama ba tareda ya jira wani ya yi mashi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Kara Kudin Ruwa Na Bashi A Nijeriya

Next Post

Hanyoyin Tsuke Gaba Wato Matsi?

Related

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 days ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 days ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

2 weeks ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

3 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

3 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

3 weeks ago
Next Post
Hanyoyin Tsuke Gaba Wato Matsi?

Hanyoyin Tsuke Gaba Wato Matsi?

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.