• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Rashin Tsaftar Muhalli A Nijeriya

by Leadership Hausa
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Kalubalen Rashin Tsaftar Muhalli A Nijeriya

A kwanan baya ne, asusun da ke tallafa wa kananan yara na Majalisar dinkin Duniya wato UNICEF, ya bayyana cewa,’yan Nijeriya sama da miliyan 95 ba a samar masu da kayan kulawa da muhalli ba.

Wannan adadin ya nuna yadda a zahiri ake ci gaba da fuskantar kalubalen rashin kula da kiwon lafiyar al’ummar kasar nan.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mbappe Lokaci Domin Dawowa Kan Ganiyarsa – Ancelotti 

A gafe daya kuma, ana ci gaba da fuskanar matsalar dabi’ar yin bahaya a fili tare da matsalar rashin samar da kayan da za a rinka kulawa da muhalli a kasar.

Wannan kididdigar ta kara jefa fargaba a cikin zukatan al’umma da kuma karya wa jama’a kwarin Gwiwa.

Babban abin takaici anan shi ne, yau a Nijeriya kimanin ‘yan kasar kimanin miliyan 48 ciki har da yara kimanin miliyan 18, sun rungumi dabi’ar yin bahaya a fili.

Labarai Masu Nasaba

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Kazalika ma, wannan matsalar har ta kai ga ta zama wata babbar annobar da ke shafar kiwon lafiyar jama’a, shafar ilimin su na zamani da kuma bunkasar tattalin arzikin al’ummar kasar, inda wannan kalubalen har ya kai ga zarce fiye da tunanin dan Adam. Bugu da kari, wasu makarantun gwamnati a kasar, da cibiyoyin kula da kiwon lafiya, musamman na gwamnatin, wadanda ya kamata ace, ana samar da inganataccen ilimin zamani su kuma cibiyoyin kiwon lafiya yadda ya kamata, amma abin bakin ciki, sun kasance tamkar kufai, saboda rashin wadata su da kayan aiki.An kiyasata cewar, makarantun Boko na gwamnati guda 91,000 da kuma cibiyoyin kula da lafiyar ‘ al’umma guda 7,600, ba a tanadar masu da kayan aiki na tsaftace muhalli ba. Hakanan ma, akan wadannan alkaluman an kiyasata cewa, ana bukatar a kalla Naira biliyan 168.75, domin a magance yin bahaya a fili a Nijeriya.

Sai dai kuma, abin takaici, anan shi ne daga shekarar 2018 zuwa 2022, Naira biliyan 15 ne kacal, aka kashe wajen magance yin bahaya a fili, wanda wannan adadin ko rabin Naira biliyan 168.75, ba su kai ba.

A jawabinsa na kwanan baya, mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima ya danganta matsalar wacce ta kara rashin tsaftar muhalli, inda ya shawarci daukacin gwamnonin jihohin kasar, da su kara zage damtse a kan kokarin da suke yi na wayar da kan al’umomin su domin a kawo karshen kalubalen yin bahaya a fili, nan da shekaru biyar masu zuwa.

Kashim ya kuma kara da cewa, wayar da kan al’umma na da matukar mahimmanci, domin ta hakan ne tamkaran dauki wani mataki na kawo karshen yin bahaya a fili, wanda hakan kuma zai inganta kiwon lafiyar ‘yan Nijeriya.

Kazalika ma, domin a yaki wannan dabi’ar ta yin bahaya a fili, gwamnatin tarayya ta samar da wani shirin tsaftace Nijeriya mai taken ‘Yin Amfani Da Bandaki Domin Wayar Da Kai.

Sai dai kash!, abin bakin cikin shi ne, ya zuwa yanzu dai, wannan shirin ya fara tafiya ne da kafar hagu saboda kuwa, a kananan hukumomi 17 a cikin dari kacal ne wannaan shirin ya samu nasara, inda kashi tara daga cikin dari, wanda jihohin kasar ke samun tallafin UNICEF.

Tun a shekarar 2023 ne gwamnatin tarayya ta samar da dauki na samar da kayan aikin kulawa da muhalli.

A namu ra’ayin a nan shi ne, dole ne gwamnonin kasar nan su dauki wannan lamarin da matukar mahimmanci.

Gudanar da gangamin wayar da kai kan batun na bukatar matukar a mayar da hankali ta yadda ya kamata, musamman a matakin gwamnatin tarayya.

Bugu da kari, ya zama dole suma sauran matakan gwamnati na jihohi da kuma kananan hukumomi, su zuba hannun jari a batun kare muhalli saboda a samar a makoma mai kyau ga Nijeriya a nan gaba.

Wata babbar illa ga rayuwar jama’a ita ce yin bahaya a fili na shafar ruwan sha da kuma yada cututtuka a cikin al’umma, tare da janyo illa ga rayuwar mata da ‘yan mata.

Kazalika, matsalar na kuma shafar fannonin ilimin zamani da tattalin arziki.

Sai dai, wata jami’a a UNICEF Rebecca Gebriel, ta na da yakinin cewa kafin nan da shekara ta 2030, daukacin jihohin kasar nan a karkashin shirin muradun karnin za su cimma burin su na yakar yin bahaya a fili.

Amma kafin a cimma wannan burin akwai matukar bukatar al’umma, kungiyoyi, kamfanoni masu zaman kansu, su sadaukar da kai.

A namu ra’ayin muna ganin ya zama wajibi ne a zuba hannun jari wajen samar da kayan tsaftace muhalli a illahirin kasar nan.

Tags: MuhalliTsafta
ShareTweetSendShare
Leadership Hausa

Leadership Hausa

Related

Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

2 hours ago
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

10 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

1 day ago
Next Post
Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) II

Darasi Na Biyu A Kan Matan Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Kwale-kwale

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

October 6, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.