• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Rashin Tsaftar Muhalli A Nijeriya

by Leadership Hausa
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Kalubalen Rashin Tsaftar Muhalli A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne, asusun da ke tallafa wa kananan yara na Majalisar dinkin Duniya wato UNICEF, ya bayyana cewa,’yan Nijeriya sama da miliyan 95 ba a samar masu da kayan kulawa da muhalli ba.

Wannan adadin ya nuna yadda a zahiri ake ci gaba da fuskantar kalubalen rashin kula da kiwon lafiyar al’ummar kasar nan.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mbappe Lokaci Domin Dawowa Kan Ganiyarsa – Ancelotti 

A gafe daya kuma, ana ci gaba da fuskanar matsalar dabi’ar yin bahaya a fili tare da matsalar rashin samar da kayan da za a rinka kulawa da muhalli a kasar.

Wannan kididdigar ta kara jefa fargaba a cikin zukatan al’umma da kuma karya wa jama’a kwarin Gwiwa.

Babban abin takaici anan shi ne, yau a Nijeriya kimanin ‘yan kasar kimanin miliyan 48 ciki har da yara kimanin miliyan 18, sun rungumi dabi’ar yin bahaya a fili.

Labarai Masu Nasaba

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

Kazalika ma, wannan matsalar har ta kai ga ta zama wata babbar annobar da ke shafar kiwon lafiyar jama’a, shafar ilimin su na zamani da kuma bunkasar tattalin arzikin al’ummar kasar, inda wannan kalubalen har ya kai ga zarce fiye da tunanin dan Adam. Bugu da kari, wasu makarantun gwamnati a kasar, da cibiyoyin kula da kiwon lafiya, musamman na gwamnatin, wadanda ya kamata ace, ana samar da inganataccen ilimin zamani su kuma cibiyoyin kiwon lafiya yadda ya kamata, amma abin bakin ciki, sun kasance tamkar kufai, saboda rashin wadata su da kayan aiki.An kiyasata cewar, makarantun Boko na gwamnati guda 91,000 da kuma cibiyoyin kula da lafiyar ‘ al’umma guda 7,600, ba a tanadar masu da kayan aiki na tsaftace muhalli ba. Hakanan ma, akan wadannan alkaluman an kiyasata cewa, ana bukatar a kalla Naira biliyan 168.75, domin a magance yin bahaya a fili a Nijeriya.

Sai dai kuma, abin takaici, anan shi ne daga shekarar 2018 zuwa 2022, Naira biliyan 15 ne kacal, aka kashe wajen magance yin bahaya a fili, wanda wannan adadin ko rabin Naira biliyan 168.75, ba su kai ba.

A jawabinsa na kwanan baya, mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima ya danganta matsalar wacce ta kara rashin tsaftar muhalli, inda ya shawarci daukacin gwamnonin jihohin kasar, da su kara zage damtse a kan kokarin da suke yi na wayar da kan al’umomin su domin a kawo karshen kalubalen yin bahaya a fili, nan da shekaru biyar masu zuwa.

Kashim ya kuma kara da cewa, wayar da kan al’umma na da matukar mahimmanci, domin ta hakan ne tamkaran dauki wani mataki na kawo karshen yin bahaya a fili, wanda hakan kuma zai inganta kiwon lafiyar ‘yan Nijeriya.

Kazalika ma, domin a yaki wannan dabi’ar ta yin bahaya a fili, gwamnatin tarayya ta samar da wani shirin tsaftace Nijeriya mai taken ‘Yin Amfani Da Bandaki Domin Wayar Da Kai.

Sai dai kash!, abin bakin cikin shi ne, ya zuwa yanzu dai, wannan shirin ya fara tafiya ne da kafar hagu saboda kuwa, a kananan hukumomi 17 a cikin dari kacal ne wannaan shirin ya samu nasara, inda kashi tara daga cikin dari, wanda jihohin kasar ke samun tallafin UNICEF.

Tun a shekarar 2023 ne gwamnatin tarayya ta samar da dauki na samar da kayan aikin kulawa da muhalli.

A namu ra’ayin a nan shi ne, dole ne gwamnonin kasar nan su dauki wannan lamarin da matukar mahimmanci.

Gudanar da gangamin wayar da kai kan batun na bukatar matukar a mayar da hankali ta yadda ya kamata, musamman a matakin gwamnatin tarayya.

Bugu da kari, ya zama dole suma sauran matakan gwamnati na jihohi da kuma kananan hukumomi, su zuba hannun jari a batun kare muhalli saboda a samar a makoma mai kyau ga Nijeriya a nan gaba.

Wata babbar illa ga rayuwar jama’a ita ce yin bahaya a fili na shafar ruwan sha da kuma yada cututtuka a cikin al’umma, tare da janyo illa ga rayuwar mata da ‘yan mata.

Kazalika, matsalar na kuma shafar fannonin ilimin zamani da tattalin arziki.

Sai dai, wata jami’a a UNICEF Rebecca Gebriel, ta na da yakinin cewa kafin nan da shekara ta 2030, daukacin jihohin kasar nan a karkashin shirin muradun karnin za su cimma burin su na yakar yin bahaya a fili.

Amma kafin a cimma wannan burin akwai matukar bukatar al’umma, kungiyoyi, kamfanoni masu zaman kansu, su sadaukar da kai.

A namu ra’ayin muna ganin ya zama wajibi ne a zuba hannun jari wajen samar da kayan tsaftace muhalli a illahirin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MuhalliTsafta
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Babban Taron Kirkire-Kirkiren Kimiyya Da Fasaha Na 2024 A Shanghai

Next Post

Darasi Na Biyu A Kan Matan Annabi (SAW)

Related

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

1 hour ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

4 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

22 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

2 days ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

3 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

3 days ago
Next Post
Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) II

Darasi Na Biyu A Kan Matan Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.