ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Malamar Jami'a

Wata Malamar Jami’ar Oyo da ke jihar Akwa Ibom, Misis Christiana Pam, ta ce domin samun abincin da za ta rayu a irin wannan lokacin da kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ke ci gaba da gudanar da yajin aiki, a yanzu haka ta rungumi sana’ar sayar da Dankalin Turawa domin samun abin kai wa baki. 

A ranar 14 ga watan Fabrairu ne kungiyar ASUU ta tsunduma yajin aikin makonni hudu a matsayin gargadi bisa bukatun da suke, daga bisa ta kara tsawaita yajin aikin zuwa wasu watanni biyu a ranar 14 ga watan Maris. Sannan ta sake sanar da wasu karin makonni 12 a ranar 9 ga watan Mayu.

  • Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo
  • Wasu Gwamnatocin Kasashe Sun Nanata Matsayinsu Na Tsaiwa Tsayin Daka Kan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Yajin aikin kamar yadda kungiyar ta ce, ta shiga ne sakamakon kasa ciki mata alkawuran da suka yi da Gwamnatin tarayya dangane da wasu tilin bukatun da take da su.

ADVERTISEMENT

A hirarta da majiyarmu bayan da hotunan ta suka karade kafafen sadarwar zamani da ke nunata tana sana’ar, Pam ta ce, ta shiga halin matsatsi na rashin kudi sakamakon ita sabuwar ma’aikaciya ce wacce ba ta samu damar tara kudade masu yawan da za ta iya rayuwa muddin yajin aikin ya jima ba.

“Lokacin da aka ayyana yajin aikin wata guda, na yi tsammanin cewa ba za a wuce wannan lokacin ba za a dawo. Na dauka cewa kungiyar ASUU da gwamantin za su samu fahimtar juna kan bukatun ASUU, kwatsam sai kuma hakan ba ta faru ba, a takaice dai aka tsawaita yajin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

A lokacin ne na fahimci tabbas ina bukatar daukan wani mataki. A farko-farkon yajin aikin na yi ta kashe kudade saboda ni sabuwa ce a lamarin don haka ban samu damar tara kudade masu yawan da zan iya rike kaina a lokacin yajin aikin ba. Bisa wannan dalilin sai na koma garinmu na asali jihar Filato domin neman mafita.

Na zo na shiga cikin matsalar kudi kai sai da aka zo gabar da ina cin bashi domin na samu yadda zan rike kaina da iyayena.

“Iyayena sun rungumi sana’ar noma hannu biyu-biyu tun ma kafin su yi ritaya a wajen aikinsu, don haka bayan da suka yi ritaya din ma sun cigaba da harkokinsu na noma. A lokacin da na koma gida, na bi su muka shiga harkar noma da tunanin cewa bayan wasu ‘yan makonni za a janye yajin aikin, sai ya zama tunanina na neman zama kamar abun wasa. Na shiga noman tare da iyayena muka share gona, aka yi shuka aka fara girbi har yanzu dai muna gida yajin aiki bai kare ba.

“Kan hakan na fara kokarin tunanin mene ne zan yi da zai ke kawo min kudin shiga ba kuma zan iya tambayar iyayena da suka yi ritaya kudi ba saboda su ma kansu suna fatan samu daga gareni. Daga bisani sai na yanke shawarar cewa na dukufa wajen Saida wasu daga cikin Dankalin da muka noma a gonarmu kuma na san za su yi daraja a Akwa Ibom.

“Da fari na fara saida Dankalin a Jos domin tara kudaden da zan yi jigilar Dankalin Uwa Akwa Ibom. Ta hakan na fara neman yadda zan rike kaina wannan dalilin ne ya sanya na shiga sana’ar saida Dankalin gadan-gadan.”

Da take bayani kan yadda jama’a suke fassara halin da ta shiga, ta ce ko a jikinta domin ita ta san halin da take ciki da kuma yadda za ta rufa wa kanta asiri kuma ta tsira da mutuncinta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir
Labarai

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Next Post
Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.