• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Labarai
0
Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya bukaci jiga-jigan siyasar Arewa masu yunkurin tsayawa takarar shugabancin kasa a 2027 da su kawar da burinsu su jira har zuwa 2031 lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kammala wa’adinsa na biyu.

Akume dai ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya halakar da tunaninsa na karbar mulki a shekarar 2027, inda ya ce idan Allah ya nufa zai zama shugaban, to zai iya lashe zabe ne kawai yana da shekaru 90 a duniya.

  • Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF
  • Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Tare Da Ƙona Gidaje A Gombe

Akume, wanda ya yi magana a ranar Lahadin da ta gabata yayin wani shiri na TBC kan harkokin siyasa, ya ce har yanzu lokaci ne na Kudu wajen samar da shugaban kasa a 2027.

Sakataren gwamnatin tarayya wanda tsohon gwamnan Jihar Benuwai ne, ya ce Shugaba Tinubu bai rasa goyon bayan ‘yan Nijeriya ba, sakamakon kudirin gyara dokar haraji da sauran tsare-tsarensa na tattalin arziki da aka dauka a cikin watanni 17 na gwamnatinsa, ya kuma bayyana fatansa na cewa Tinubu zai jagoranci Nijeriya har na tsowon shekaru 8.

Ya kare kudirin sake fasalin haraji a matsayin wasu tsare-tsare masu kyau da za su taimaki kasar nan idan har majalisar dokoki ta amince da su.

Labarai Masu Nasaba

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

Ya ce, “Ya kamata a bar Shugaba Tinubu a matsayinsa na dan Kudu ya sake yin wa’adi na biyu, ma’ana wadanda ke sa ido a kan smun shugabanci daga Arewa a 2027 su jira har 2031.

“Idan har Allah ya nufa Alhaji Atiku Abubakar zai zama shugaban Nijeriya, ko da yana da shekara 90, zai iya samun haka. Amma shi da sauran ’yan Arewa da ke sa ido kan ofishin shugaban kasa a 2027 su jira har Tinubu ya kammala wa’adinsa karo na biyu.”

Akume ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su kyale kudirin dokar sake fasalin haraji su daidaita ta hanyoyin da ake bukata na majalisa, yana mai cewa, “Suna da kyakkyawar manufa ga Nijeriya da ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamitin Amintattun PDP Ya Dage Kan Mika Shugabancin Jam’iyyar Ga Sashin Arewa Ta Tsakiya

Next Post

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Related

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

3 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

5 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

8 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

11 hours ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

21 hours ago
Next Post
Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

May 24, 2025
Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

May 24, 2025
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

May 24, 2025
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

May 24, 2025
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

May 24, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

May 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.