• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Lamunci Masu Zagon Kasa Su Durkusar Da Masana’antu Ba

by Bello Hamza
7 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Lamunci Masu Zagon Kasa Su Durkusar Da Masana’antu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwmnatin Tarayya ta yi kira ga masu ruwa da tsaki da shugabanni a fannin masana’antu, da su gudanar da shugabanci na gari tare da tabbatar da bin ka’ida, musamman domin a kara a habaka arzikin da ke a cikin nahiyar Afirka.

A cewar Gwamnatin, ba za ta kwale masu zagon kasa ko masu wata manufa su tarwatsa masana’antar ba.

  • Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista
  • Dalilan Da Suka Sa Gwamnan Kano Sallamar SSG Da Wasu Kwamishinoni 5

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya sanar da haka a jawabinsa a taron kaddamar da baje koli na kasa da kasa IEEER da aka gudanar a Abijan, Babban Birinin Kasar Coded’boire.

Kazalika, Shetrima ya bayyana cewa, wasu masu sanya ra’ayin kashin kansu a fannin gudanar da masana’antu ne ke janyo akuwar kalubale ga fannin da kuma janyo haddasa aukuwar rikice-rikice a yankunan da ke da albarkatun danyen mai

Shettima ya ci gaba da cewa, “Ba zan rungume hannu mu kyale irin wadannan masu yiwa fannin na masana’antu, zagon kasa ba, musamman don kar su samu damar cika burinsu”.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Mataikin ya kara da cewa, domin a takawa irin wadannan masu zagon kasar birki ne, Nijeriya ta samar da wani tsari na musamman domin a bai wa yankunan da ake hakar ma’adainai na kasar kariyar da ta kamata, musamman don a kara habaka fannin na ma’adanan kasar.

Ya sanar da cewa, Nijeriya Allah ya albarkace ta da Gwal da ya kai kashi 40 a cikin dari a fadin duniya.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa, Nijeriya na da yawan mai da ya kai kashi 10 a ciin dari, tare da kuma albarkatun kasa kamar irinsucobalt da lithium.

Sai dai, ya bayyana cewa, akwai irin wadannan albakatun kasar da har yanzu, ba a riga an tono su ba.

Mataimakin ya kuma bayar da tabbacin cewa, Nijeriya za ta ci gaba kula da masana’antun kasar, musamman domin a tabbatar da bin ka’ida da yin hadaka a kan kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan.

Taken taron shi ne, “Samar da Tsare-Tsare domin a kara habaka kayan da ake sarrafawa da kuma kula da masana’antar samar da makamashi”.

Shugabani da suka fito daga kasashen Afrika da dama ne suka halarci taron domin su tattauna kan yadda za su lalubo da mafita a fannin kirkier-kirkire da kuma kara kula da fannin samar da makamashi.

A cewar Mataimakin Shugaban kasar ba wai kawai ana magana ne a kan albarkatun kasa ba, batun ya kuma hada da yadda za a inganta rayuwar alumma da kuma samar masu da turba mai dorewa.

Ya sanar da cewa, idan aka samar da tsare-tsaren da suka kamata da bin ka’ida da kuma tabbatar da gaskiya, za a iya samun damar bunkasa fannin samar da mai mai makon kawo rabuwar kawuna.

Shettima ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya a cikin sauye-sauyen da ta samar da ta kara habaka ayyukan Hukumar dake sa ido kan albarkatun ma’adanai ta kasa, wato NEITI.

Kazalika, Shettima ya bayar da tabbacin cewa, akwai bukatar kasashen da ke a nahiyar Afrika da ke fuskantar kalubale iri daya da su mayar da hankali wajen lalubo da hanyoyin magance kalubalen.

Mataimakin Shugaban kasar ya sanar da cewa, sake samar da sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ta yi a kamfanin man fetur na kasa NNPCL a karkashin dokar da ke tafiyar da masana’antar sarrafa man fetur ta 2021, hakan ya sanya kamfanin ya mayar da hankali wajen hada-hadar kasuwanci man wanda hakan ya kara habaka fannin na man.

Ya sanar da cewa, a yanzu kamfnin na NNPC, na gudanar da ayyukansa ne kai tsaye, ba tare da shishigin bangaren Gwamnatin Tarayya ba.

Mataimakin Shugaban kasar ya kuma jaddada mahimmancin gudunmawa kayan da ake sarrafawa a kasar suke da shi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Shettima ya sanar da cewa, ta hanyar dokar kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan ta 2010, Nijeriya ta samu damar kara shiga fannin samar da man fetur da iskar Gas wanda ya kai daga kashi 5 a cikin dari, zuwa kashi 30 a cikin dari.

Ya sanar da cewa, bisa nasarar da aka samu ta kafa matatar mai ta Dangote wacce kuma ta kasance mafi girma, a hakan ya sanya Nijeriya za ta iya kara mayar da hankali wajen sarafa kayan cikin gida.

Shi ma a na sa jawabin a wajen taron Mataimakin Shugaban kasar Côte d’Iboire, Tremoko Meyliet Kone, ya bayyana jin dadinsa kan ziyarar aikin da Shettima da sauran baki da suka halarci taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Shettima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN : Sin Ta Shirya Cimma Burin Samun Ci Gaba Na Shekara-Shekara, Masu Bayyana Ra’ayoyinsu Na Da Karfin Gwiwa Game Da Hasashen Tattalin Arzikin Sin

Next Post

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

19 minutes ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

4 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

6 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

7 hours ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

16 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

18 hours ago
Next Post
Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.