ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Lamunci Masu Zagon Kasa Su Durkusar Da Masana’antu Ba

by Bello Hamza
2 years ago
Gwamnatin

Gwmnatin Tarayya ta yi kira ga masu ruwa da tsaki da shugabanni a fannin masana’antu, da su gudanar da shugabanci na gari tare da tabbatar da bin ka’ida, musamman domin a kara a habaka arzikin da ke a cikin nahiyar Afirka.

A cewar Gwamnatin, ba za ta kwale masu zagon kasa ko masu wata manufa su tarwatsa masana’antar ba.

  • Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista
  • Dalilan Da Suka Sa Gwamnan Kano Sallamar SSG Da Wasu Kwamishinoni 5

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya sanar da haka a jawabinsa a taron kaddamar da baje koli na kasa da kasa IEEER da aka gudanar a Abijan, Babban Birinin Kasar Coded’boire.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Shetrima ya bayyana cewa, wasu masu sanya ra’ayin kashin kansu a fannin gudanar da masana’antu ne ke janyo akuwar kalubale ga fannin da kuma janyo haddasa aukuwar rikice-rikice a yankunan da ke da albarkatun danyen mai

Shettima ya ci gaba da cewa, “Ba zan rungume hannu mu kyale irin wadannan masu yiwa fannin na masana’antu, zagon kasa ba, musamman don kar su samu damar cika burinsu”.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Mataikin ya kara da cewa, domin a takawa irin wadannan masu zagon kasar birki ne, Nijeriya ta samar da wani tsari na musamman domin a bai wa yankunan da ake hakar ma’adainai na kasar kariyar da ta kamata, musamman don a kara habaka fannin na ma’adanan kasar.

Ya sanar da cewa, Nijeriya Allah ya albarkace ta da Gwal da ya kai kashi 40 a cikin dari a fadin duniya.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa, Nijeriya na da yawan mai da ya kai kashi 10 a ciin dari, tare da kuma albarkatun kasa kamar irinsucobalt da lithium.

Sai dai, ya bayyana cewa, akwai irin wadannan albakatun kasar da har yanzu, ba a riga an tono su ba.

Mataimakin ya kuma bayar da tabbacin cewa, Nijeriya za ta ci gaba kula da masana’antun kasar, musamman domin a tabbatar da bin ka’ida da yin hadaka a kan kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan.

Taken taron shi ne, “Samar da Tsare-Tsare domin a kara habaka kayan da ake sarrafawa da kuma kula da masana’antar samar da makamashi”.

Shugabani da suka fito daga kasashen Afrika da dama ne suka halarci taron domin su tattauna kan yadda za su lalubo da mafita a fannin kirkier-kirkire da kuma kara kula da fannin samar da makamashi.

A cewar Mataimakin Shugaban kasar ba wai kawai ana magana ne a kan albarkatun kasa ba, batun ya kuma hada da yadda za a inganta rayuwar alumma da kuma samar masu da turba mai dorewa.

Ya sanar da cewa, idan aka samar da tsare-tsaren da suka kamata da bin ka’ida da kuma tabbatar da gaskiya, za a iya samun damar bunkasa fannin samar da mai mai makon kawo rabuwar kawuna.

Shettima ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya a cikin sauye-sauyen da ta samar da ta kara habaka ayyukan Hukumar dake sa ido kan albarkatun ma’adanai ta kasa, wato NEITI.

Kazalika, Shettima ya bayar da tabbacin cewa, akwai bukatar kasashen da ke a nahiyar Afrika da ke fuskantar kalubale iri daya da su mayar da hankali wajen lalubo da hanyoyin magance kalubalen.

Mataimakin Shugaban kasar ya sanar da cewa, sake samar da sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ta yi a kamfanin man fetur na kasa NNPCL a karkashin dokar da ke tafiyar da masana’antar sarrafa man fetur ta 2021, hakan ya sanya kamfanin ya mayar da hankali wajen hada-hadar kasuwanci man wanda hakan ya kara habaka fannin na man.

Ya sanar da cewa, a yanzu kamfnin na NNPC, na gudanar da ayyukansa ne kai tsaye, ba tare da shishigin bangaren Gwamnatin Tarayya ba.

Mataimakin Shugaban kasar ya kuma jaddada mahimmancin gudunmawa kayan da ake sarrafawa a kasar suke da shi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Shettima ya sanar da cewa, ta hanyar dokar kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan ta 2010, Nijeriya ta samu damar kara shiga fannin samar da man fetur da iskar Gas wanda ya kai daga kashi 5 a cikin dari, zuwa kashi 30 a cikin dari.

Ya sanar da cewa, bisa nasarar da aka samu ta kafa matatar mai ta Dangote wacce kuma ta kasance mafi girma, a hakan ya sanya Nijeriya za ta iya kara mayar da hankali wajen sarafa kayan cikin gida.

Shi ma a na sa jawabin a wajen taron Mataimakin Shugaban kasar Côte d’Iboire, Tremoko Meyliet Kone, ya bayyana jin dadinsa kan ziyarar aikin da Shettima da sauran baki da suka halarci taron.

Gwamnatin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.