• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Madaciya A Jikin Dan’adam

by Sani Anwar
6 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Aikin Madaciya A Jikin Dan’adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jakar madaciya na nan danfare da hanta, daga kasan hantar a bangaren dama daga sama a cikin Dan’adam.

Hanta ce ke samar da ruwan madaciya, wadda ke da launin kore ko kuma rawayar gwal, sannan sai ruwan madaciyar ya gangaro zuwa cikin jakar madaciya; domin ajiya zuwa lokacin da za a bukace shi.

  • Dalilai 15 Na Muhimmancin Tsara Yadda Malami Zai Koyar Da Darussa A Aji (2)
  • Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Tare Da Ƙona Gidaje A Gombe

Kazalika, Hanta na iya samar da ruwan madaciya da yawansa ya kai kimanin lita 800 zuwa 1200 a kullum. A yayin da jakar madaciyar ke iya cin ruwan madaciyar da yawansa ya kai lita 50 bayan ta tace mafi yawan ruwan da ke ciki.

Har ila yau, ruwan madaciya ya kunshi kashi 97.6 cikin 100 ruwa zalla da kuma kashi 2.4 cikin 100 na gishirin madaciya da sauran burbishin ma’adanai da sauran makamantansu.

Gishirin madaciya shi ne jigon aikin madaciya a jikin Dan’adam, musamman wajen narka abinci da mutum ya ci.

Labarai Masu Nasaba

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Haka zalika, gishirin madaciya shi ne jigon sinadarin da ke narka ko markada abinci a ajin mai ko kitse a cikin karamin hanji, har a mayar da shi zuwa yadda jiki zai iya zukar sa daga karamin hanji zuwa sassan jiki.

Bugu da kari, gishirin madaciya na taimakawa wajen yi wa hanta kaimi; don samar da ruwan madaciya a jikin mutum.

Har wa yau, gishirin madaciya na taimakawa wajen saukaka fitowar bayan-gida daga cikin babban hanji zuwa dubura. Haka kuma, daga cikin ruwan madaciyar ne bayan-gida ke samun launi irin na ruwan kasar da yake da shi.

Tsakuwar madaciya: A yayin da kwalastirol ko kitse ya yi yawa a jikin mutum, kwalastirol din na iya curewa wuri guda ya haifar da matsalar da ake cewa; tsakuwar madaciya wato ‘gallstone’ a turance. Gishirin madaciya na taimakawa wajen magance curewar kwalastirol a cikin jakar madaciyar da ke jikin Dan’adam.

Haka zalika, duk da dimbin alfanun da madaciya ked a shi a jikin Dan’adam, ana iya yin tiyata a cire jakar madaciyar idan aka samu matsalar tsakuwar madaciya; sannan kuma a gaza samun magungunan da za su magance cutar tsakuwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Abba Ya Umarci Kwamishinonin Da Ya Sauyawa Ma’aikatu Su Fara Aiki A Ranar Talata

Next Post

Gyaran Kafa Don Maganin Faso Da Kaushi

Related

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

1 week ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

1 week ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

4 weeks ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

1 month ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

2 months ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Next Post
Gyaran Kafa Don Maganin Faso Da Kaushi

Gyaran Kafa Don Maganin Faso Da Kaushi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.