• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabaru Da Fasahohin Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Wajen Tinkarar Kwararar Hamada

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Hamada

Rumfar kasar Sin a taron kasashen da suka kulla yarjejeniyar hana kwararar hamada ta MDD karo na 16 wato COP 16, ta gudanar da karamin taro a kwanan baya, mai taken“Fasahar kiyaye muhalli da makoma mai kyau”, inda kasar Sin ta yi musayar dabarun samun ci gaban hadin gwiwarta da sauran kasashe a bangaren hana yaduwar hamada. A hakika dai, har kullum Sin na bude kofarta ga sauran kasashe kan more dabarar hana kwararar hamada, don samar da gudummawarta ga kasashen da suka yi fama da wannan matsala.

 

Afirka nahiya ce da ta fi fama da kwararar hamada a duniya, hukumar kiyaye muhalli ta MDD ta ba da alkaluma cewa, filayen da yawansu ya kai kashi 45% na fadin nahiyar Afirka na fama da kwararar hamada a mabambantan matakai. Don kare kwararar hamada, kasashen Afirka na gudanar da jerin shirye-shirye, musamman ma shirin “babbar ganuwar itatuwa ta Afirka ”.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Muhimmin Taron Tattalin Arziki Don Tsara Ayyukan 2025
  • Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista

Don tallafa wa kasashen Afirka a kokarinsu na hana kwararowar hamada, Kasar Sin ta sha gudanar da kwasa-kwasai din horar da kwararrun kasashen Afrika dangane da wannan shiri. A shekarar 2017 kuma, cibiyar nazarin yanayin halittu da yanayin kasa ta jihar Xinjiang ta kasar Sin ta kulla yarjejeniyar fahimtar juna da sakatariyar kungiyar babbar ganuwar itatuwa ta Afirka, ta yadda za su yi hadin gwiwa a bangaren sa ido kan tsarin muhallin halittu da amfani da albarkatun kasa cikin dorewa da horar da kwararru da samar da fasaha da sauransu, don kara karfin kasashen Afirka wajen yaki da kwararar hamada. A jihar Kano na Najeriya, cibiyar nazari ta hadin kan Sin da Afirka ta yi nazari kan matsalolin da ake fuskanta a wurin, ta kafa sabon salon shingen kare kwararar hamada da yankin gwaji na dasa itatuwan dake iya samar da arziki. Duba da iyakacin kokarin da Sin da kasashen Afirka suke yi, kason hamada a yankin Sahel ya ragu daga kashi 72.31% na shekarar 2000 zuwa kashi 69.23% na shekarar 2020.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Dabarar da Sin take samu da ma fasahar zamani da take da ita, ababen bukata ne ga Afirka tamkar ruwa a jallo wajen dakile kwarar hamada, an yi imanin cewa, kasashen Afirka za su kara karfinsu na daidaita muhallin halittu da samun bunkasuwa mai dorewa bisa fasahar zamani iri na kasar Sin, da aiwatar da manufofin Sin bisa yanayin da suke ciki. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Next Post
Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.