ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

by Abubakar Abba
1 year ago
Tarayya

Babbar Kotun Tarayya mai lamba daya dake da zamanta a Jihar Kaduna Daura da ND, wacce mai Shari’a R.M. Aikawa, ke alkalanci, ta fara sauraran karar da wasu mahajjatan shekara ta 2024 su 64.

Mahajjatan sun dai maka Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ne tare da Hukumar Alhazain ta Jihar Kaduna a kan wasu hakkokinsu, da ba su cika musu ba a ya yin da suke gudanar da aikin hajjin na 2024.

  • Hajji 2025: NAHCON Ta Tantance Kamfanonin Jiragen Da Za Su Yi Jigilar Alhazai Zuwa Saudiyya
  • Kotu Ta Bayar Da Belin Yahaya Bello Kan Naira Miliyan 500

A hirarsa da manema labarai jim kadan bayan tashi daga zaman kotun, Barista Bashir Musa lauyan masu kara ya ce, “ Mun zo kotu ne, sakamakon mutanen da muke tsayawa a matsayin su na mahajjata da suka biya kudaden su na zuwa aikin hajji ta karkashin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna na shekarar 2024.”

ADVERTISEMENT

Ya ce, wadanda muka tsayawa, sun rubuta wata takarda, suna bukatar sanin yadda aka yi kudadensu aka kashe su a lokacin aikin hajjin na 2024, ga su hukumar aikin hajji ta kasa da kuma ta Jihar Kaduna, wato suna bukatar wadannan hukumomin biyu, su bayani ta yaya aka yi da kudadensu da kuma yadda aka yi da Naira biliyan 90 wanda Gwamnatin Tarayya ta bayar a matsayin kudin tallafi na aikin hajjin na 2024, sakamakon yanayin yadda aka yi musu a Saudiyya, yadda aka karbe su a Saudiyya da yadda suka gabatar da aikin na su.”

Bashir ya ci gaba da cewa,“Wadnda muke tsayawar, akwai tambayoyi da suke da su akan yadda aka yi da wannan kudin, saboda ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba a lokacin da suka kaddamar da aikin hajjin.”

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya kara da cewa, da suka rubuta, har zuwa yau, an bayar da kwanuka 30 ga wadannan hukumomin, amma ba su iya bayar da wadannan bayanai a rubuce ba, shi ya sa muka garzaya zuwa kotu, domin kotun ta sanya su, na farko dai, muna son mu sani daga kotun shin ma muna da ‘yanci? To kotu ta sanya su tilas hukumomin su bayar da wadannan dalilan a kan yadda aka yi da wadannan kudaden a rubuce.

Ya sanar da cewa, wadanda suka shigar karar su 64 ne, domin wadannan bukatun, inda ya ce, iya sanin mu a cikin wadannan masu karar  kowanne daya babu wanda ya biya kasa da Naira miliyan shida da dari shida da ‘yan kai na aikin hajjin na bana.

Bashir ya sanar da cewa, a zaman farko da kotun ta yi kan karar, amma Lauyan hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar Kaduna suka aiko da takarda, suna bukatar a daga musu zuwa zaman kotun na gaba domin a yanzu suna gaban wata kotu, mu kuma ganin cewa wannan ne zama na farko sai muka ba su uzuri ba mu kalubalanci bukatar su ba, amma muna so su zo mu zauna, aji muhawarar ko wanne bangare.

A cewrsa, “ Fatanmu shi ne, su kawo dalilan da suka hana su duba wannan takarda da muka rubuta musu wanda kuma a karshe muna son kotu ta duba, idan wannan yanayin ya bukaci a sanya su su biya mu wasu kudade na wahalhalun da muka sha kotu ta sanya su su biya mu.

Kotun ta sanya ranar 21 na watan Janairu 2025 domin a dawo a saurari wannan sharia’ar.

Tarayya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.