ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

by Abubakar Abba
2 years ago
Tarayya

Babbar Kotun Tarayya mai lamba daya dake da zamanta a Jihar Kaduna Daura da ND, wacce mai Shari’a R.M. Aikawa, ke alkalanci, ta fara sauraran karar da wasu mahajjatan shekara ta 2024 su 64.

Mahajjatan sun dai maka Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ne tare da Hukumar Alhazain ta Jihar Kaduna a kan wasu hakkokinsu, da ba su cika musu ba a ya yin da suke gudanar da aikin hajjin na 2024.

  • Hajji 2025: NAHCON Ta Tantance Kamfanonin Jiragen Da Za Su Yi Jigilar Alhazai Zuwa Saudiyya
  • Kotu Ta Bayar Da Belin Yahaya Bello Kan Naira Miliyan 500

A hirarsa da manema labarai jim kadan bayan tashi daga zaman kotun, Barista Bashir Musa lauyan masu kara ya ce, “ Mun zo kotu ne, sakamakon mutanen da muke tsayawa a matsayin su na mahajjata da suka biya kudaden su na zuwa aikin hajji ta karkashin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna na shekarar 2024.”

ADVERTISEMENT

Ya ce, wadanda muka tsayawa, sun rubuta wata takarda, suna bukatar sanin yadda aka yi kudadensu aka kashe su a lokacin aikin hajjin na 2024, ga su hukumar aikin hajji ta kasa da kuma ta Jihar Kaduna, wato suna bukatar wadannan hukumomin biyu, su bayani ta yaya aka yi da kudadensu da kuma yadda aka yi da Naira biliyan 90 wanda Gwamnatin Tarayya ta bayar a matsayin kudin tallafi na aikin hajjin na 2024, sakamakon yanayin yadda aka yi musu a Saudiyya, yadda aka karbe su a Saudiyya da yadda suka gabatar da aikin na su.”

Bashir ya ci gaba da cewa,“Wadnda muke tsayawar, akwai tambayoyi da suke da su akan yadda aka yi da wannan kudin, saboda ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba a lokacin da suka kaddamar da aikin hajjin.”

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Ya kara da cewa, da suka rubuta, har zuwa yau, an bayar da kwanuka 30 ga wadannan hukumomin, amma ba su iya bayar da wadannan bayanai a rubuce ba, shi ya sa muka garzaya zuwa kotu, domin kotun ta sanya su, na farko dai, muna son mu sani daga kotun shin ma muna da ‘yanci? To kotu ta sanya su tilas hukumomin su bayar da wadannan dalilan a kan yadda aka yi da wadannan kudaden a rubuce.

Ya sanar da cewa, wadanda suka shigar karar su 64 ne, domin wadannan bukatun, inda ya ce, iya sanin mu a cikin wadannan masu karar  kowanne daya babu wanda ya biya kasa da Naira miliyan shida da dari shida da ‘yan kai na aikin hajjin na bana.

Bashir ya sanar da cewa, a zaman farko da kotun ta yi kan karar, amma Lauyan hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar Kaduna suka aiko da takarda, suna bukatar a daga musu zuwa zaman kotun na gaba domin a yanzu suna gaban wata kotu, mu kuma ganin cewa wannan ne zama na farko sai muka ba su uzuri ba mu kalubalanci bukatar su ba, amma muna so su zo mu zauna, aji muhawarar ko wanne bangare.

A cewrsa, “ Fatanmu shi ne, su kawo dalilan da suka hana su duba wannan takarda da muka rubuta musu wanda kuma a karshe muna son kotu ta duba, idan wannan yanayin ya bukaci a sanya su su biya mu wasu kudade na wahalhalun da muka sha kotu ta sanya su su biya mu.

Kotun ta sanya ranar 21 na watan Janairu 2025 domin a dawo a saurari wannan sharia’ar.

Tarayya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.