• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sokoto Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan 15 Ga Gyaran Makarantu, Motocin Alkalai Da Sauransu 

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Sokoto Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan 15 Ga Gyaran Makarantu, Motocin Alkalai Da Sauransu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da kashe naira biliyan 15 domin gyaran makarantu da samar da motoci a hukumance ga alkalan manyan kotuna da Khadis na kotunan Shari’ar Musulunci.

 

Da yake zantawa da manema labarai bayan zaman majalisar zartarwa ta jihar a ranar Alhamis, kwamishinan ilimi, Alhaji Tukur Arkali, ya ce an amince da Naira miliyan 788.2 da Naira miliyan 591.4 da kuma Naira miliyan 433.1 don gyara Kwalejin ‘Sheikh Gummi Memorial College’; makarantar sakandire ta larabci ta Hafsatu Ahmadu Bello da kuma Kwalejin fasaha ta sokoto.

  • Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Lakurawa A Sokoto Da Kebbi, Tare Da Ƙwato Makamai
  • Shugaban Sin Ya Jinjinawa Nasarorin Da Yankin Macao Ya Samu Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sauran makarantun da za a gyara sun hada da makarantar sakandire ta Unity, Bodinga a kan Naira miliyan 567,5; makarantar sakandiren Sani Dingyadi Unity, Farfaru akan Naira miliyan 374.6 da kuma cibiyar darusan karatuttukan Alkur’ani da sauran fannoni ta Sultan Maccido akan Naira biliyan 1.6

 

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

Bugu da kari, an sake amincewa da Naira biliyan 1.3 da Naira miliyan 591.4 domin gyara makarantar sakandiren mata ta gwamnati, Illela da sakandiren gwamnati illela da ambaliyar ruwa ta lalata.

 

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Alhaji Bala Kokani ya kara bayyana cewa, an amince da kudi Naira miliyan 710.6 da kuma Naira miliyan 105.8 domin gyara gine-ginen da suka ruguje a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Sakkwato da Kwalejin Ahmadu Bello da ke Farfaru.

 

Hakazalika, an amince da kashe Naira miliyan 250 da Naira miliyan 122 domin gyara gidajen ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Umaru Ali Shinkafi Sokoto, da gina katafaren bandakai guda tara a harabar makarantar.

 

Bugu da kari, majalisar ta amince da siyan motocin jeeps guda 22 (na 2024) kan kudi Naira biliyan 2.4 ga alkalan manyan kotuna da kadis na kotun Shari’ar Musulunci.

 

Kwamishinan yada labarai da wayar da kan jama’a na jihar, Alhaji Sambo Bello Danchadi, ya ce majalisar ta kuma amince da kwangilar samar da sabuwar na’urar watsa labarai ta Rima FM Sokoto da kuma gyaran antenar gidan rediyon AM da ke kan antena mai nauyin 50 (kilowatts) akan kudi Naira miliyan 926.

 

Ya kuma bayyana amincewar majalisar kan gyaran injin janareta mai karfin wuta kilowatt 2000 na hukumar kula da samar da ruwa ta jihar sokoto akan kudi naira miliyan 80,850.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Kai Tsaye Da Ba Na Kudi Ba Na Sin A Kasashen Waje Ya Karu Da 11.2% Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Related

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

4 hours ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

8 hours ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

19 hours ago
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

20 hours ago
Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

1 day ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Wutar lantarki

Arewa Maso Gabas Ce Za Ta Biya Kudin Wuta Mafi Tsada A Sabon Tsarin Lantarki

July 25, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

July 25, 2025
Manzon Allah

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

July 25, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.