ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sokoto Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan 15 Ga Gyaran Makarantu, Motocin Alkalai Da Sauransu 

by Sulaiman
2 years ago
Sokoto

Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da kashe naira biliyan 15 domin gyaran makarantu da samar da motoci a hukumance ga alkalan manyan kotuna da Khadis na kotunan Shari’ar Musulunci.

 

Da yake zantawa da manema labarai bayan zaman majalisar zartarwa ta jihar a ranar Alhamis, kwamishinan ilimi, Alhaji Tukur Arkali, ya ce an amince da Naira miliyan 788.2 da Naira miliyan 591.4 da kuma Naira miliyan 433.1 don gyara Kwalejin ‘Sheikh Gummi Memorial College’; makarantar sakandire ta larabci ta Hafsatu Ahmadu Bello da kuma Kwalejin fasaha ta sokoto.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Lakurawa A Sokoto Da Kebbi, Tare Da Ƙwato Makamai
  • Shugaban Sin Ya Jinjinawa Nasarorin Da Yankin Macao Ya Samu Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sauran makarantun da za a gyara sun hada da makarantar sakandire ta Unity, Bodinga a kan Naira miliyan 567,5; makarantar sakandiren Sani Dingyadi Unity, Farfaru akan Naira miliyan 374.6 da kuma cibiyar darusan karatuttukan Alkur’ani da sauran fannoni ta Sultan Maccido akan Naira biliyan 1.6

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Bugu da kari, an sake amincewa da Naira biliyan 1.3 da Naira miliyan 591.4 domin gyara makarantar sakandiren mata ta gwamnati, Illela da sakandiren gwamnati illela da ambaliyar ruwa ta lalata.

 

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Alhaji Bala Kokani ya kara bayyana cewa, an amince da kudi Naira miliyan 710.6 da kuma Naira miliyan 105.8 domin gyara gine-ginen da suka ruguje a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Sakkwato da Kwalejin Ahmadu Bello da ke Farfaru.

 

Hakazalika, an amince da kashe Naira miliyan 250 da Naira miliyan 122 domin gyara gidajen ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Umaru Ali Shinkafi Sokoto, da gina katafaren bandakai guda tara a harabar makarantar.

 

Bugu da kari, majalisar ta amince da siyan motocin jeeps guda 22 (na 2024) kan kudi Naira biliyan 2.4 ga alkalan manyan kotuna da kadis na kotun Shari’ar Musulunci.

 

Kwamishinan yada labarai da wayar da kan jama’a na jihar, Alhaji Sambo Bello Danchadi, ya ce majalisar ta kuma amince da kwangilar samar da sabuwar na’urar watsa labarai ta Rima FM Sokoto da kuma gyaran antenar gidan rediyon AM da ke kan antena mai nauyin 50 (kilowatts) akan kudi Naira miliyan 926.

 

Ya kuma bayyana amincewar majalisar kan gyaran injin janareta mai karfin wuta kilowatt 2000 na hukumar kula da samar da ruwa ta jihar sokoto akan kudi naira miliyan 80,850.

Sokoto
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.