ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sokoto Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan 15 Ga Gyaran Makarantu, Motocin Alkalai Da Sauransu 

by Sulaiman
2 years ago
Sokoto

Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da kashe naira biliyan 15 domin gyaran makarantu da samar da motoci a hukumance ga alkalan manyan kotuna da Khadis na kotunan Shari’ar Musulunci.

 

Da yake zantawa da manema labarai bayan zaman majalisar zartarwa ta jihar a ranar Alhamis, kwamishinan ilimi, Alhaji Tukur Arkali, ya ce an amince da Naira miliyan 788.2 da Naira miliyan 591.4 da kuma Naira miliyan 433.1 don gyara Kwalejin ‘Sheikh Gummi Memorial College’; makarantar sakandire ta larabci ta Hafsatu Ahmadu Bello da kuma Kwalejin fasaha ta sokoto.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Lakurawa A Sokoto Da Kebbi, Tare Da Ƙwato Makamai
  • Shugaban Sin Ya Jinjinawa Nasarorin Da Yankin Macao Ya Samu Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sauran makarantun da za a gyara sun hada da makarantar sakandire ta Unity, Bodinga a kan Naira miliyan 567,5; makarantar sakandiren Sani Dingyadi Unity, Farfaru akan Naira miliyan 374.6 da kuma cibiyar darusan karatuttukan Alkur’ani da sauran fannoni ta Sultan Maccido akan Naira biliyan 1.6

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Bugu da kari, an sake amincewa da Naira biliyan 1.3 da Naira miliyan 591.4 domin gyara makarantar sakandiren mata ta gwamnati, Illela da sakandiren gwamnati illela da ambaliyar ruwa ta lalata.

 

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Alhaji Bala Kokani ya kara bayyana cewa, an amince da kudi Naira miliyan 710.6 da kuma Naira miliyan 105.8 domin gyara gine-ginen da suka ruguje a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Sakkwato da Kwalejin Ahmadu Bello da ke Farfaru.

 

Hakazalika, an amince da kashe Naira miliyan 250 da Naira miliyan 122 domin gyara gidajen ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Umaru Ali Shinkafi Sokoto, da gina katafaren bandakai guda tara a harabar makarantar.

 

Bugu da kari, majalisar ta amince da siyan motocin jeeps guda 22 (na 2024) kan kudi Naira biliyan 2.4 ga alkalan manyan kotuna da kadis na kotun Shari’ar Musulunci.

 

Kwamishinan yada labarai da wayar da kan jama’a na jihar, Alhaji Sambo Bello Danchadi, ya ce majalisar ta kuma amince da kwangilar samar da sabuwar na’urar watsa labarai ta Rima FM Sokoto da kuma gyaran antenar gidan rediyon AM da ke kan antena mai nauyin 50 (kilowatts) akan kudi Naira miliyan 926.

 

Ya kuma bayyana amincewar majalisar kan gyaran injin janareta mai karfin wuta kilowatt 2000 na hukumar kula da samar da ruwa ta jihar sokoto akan kudi naira miliyan 80,850.

Sokoto
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.