• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumomi biyu da suke yaki da cin hanci da rashawa da dangoginsu wato EFCC da ICPC, sun samu nasarar kwato naira biliyan 277.685 da kuma kudin da yawansa ya kai dala miliyan 105,966 a cikin shekara daya.

Yayin da EFCC ta kwato rukunin gidaje 753, ita kuma ICPC ta bi diddingin ayyuka 1,500 a fadin kasar nan.

  • Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025
  • Yadda Minista Ya Kaddamar Da Ginin Radio House Da Aka Yi Wa Kwaskwarima A Abuja

Kazalika, ICPC ta samu nasarar dakile ma’aikatu da sashi-sashi daga taba naira biliyan 10.8 na kudaden da ba a yi amfani da su ba.

Hukumomi biyun sun samu nasarar gurfanar da mutane 3,468 da laifuka daban-daban a cikin shekara guda.

Daraktan sashin shari’a na ofishin mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro (ONSA), Zakari Mijinyawa, shi ne ya shaida hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Abuja jiya.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Mijinyawa ya ce a halin yanzu tsofaffin gwamnoni hudu da tsofaffin ministoci uku su na kan fuskar shari’a a kotuna daban-daban. Sai dai bai bayyana sunayen su ba.

Ya misalta nasarorin hukumomin biyu a matsayin wata gagarumar ci gaba da kokarin gwamnati na yaki da cin hanci da rashawa a fadin kasar nan.

“A karkashin jagorancin babban shugaba, Ola Olukoyede, EFCC ta aiwatar da sauye-sauye masu gayar ma’ana, da suka hada da kafa sabuwar sashi-sashi na yaki da ‘yan damfara, farfado da ofisoshin shiyyoyi, da kuma kafa gidan rediyon EFCC 97.3FM domin wayar da kan jama’a.

‘’Hukumar ta amshi bakwancin babban taro kan laifukan yanar gizo da masu ruwa da tsaki ciki har da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka halarta.

“Hukumar ta sashin tawagar musamman dinta ta samu nasarar gurfanar da masu laifukan 35 da suka ci zarafin Naira.

‘’A duniyance, EFCC ta samu inganta hadaka da FBI da Canadian Royal Mounted Police, da kwato kadarorin da aka boye a kasashen waje.”

Ya ce gurfanar da tsofaffin gwamnoni da ministoci ciki har da tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, kan sama da fadi da duniyar al’umma da sauran laifuka ya nuna kokarin hukumar wajen wanzar da gaskiya da adalci.

Ya ce, “Nasarorin da ICPC ya cimma a 2024 abun alfahari ne. Hukumar ta kwato tsabar kudi na naira biliyan 29.685 da dala 966,900.83, da kuma kari kan dakile ma’aikatu da sashi-sashi daga taba naira biliyan 10.8 na kudaden da ba a yi amfani da su ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

Next Post

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

4 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

5 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

10 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

12 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

13 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.