• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Na san da yawa cikin masu bibiyar alamuran dake faruwa a harkokin kasa da kasa, ba su manta da yadda a baya bayan nan kungiyar tarayyar Turai EU, ta fitar da wasu sabbin matakai na kakabawa wasu sassan kasar Sin takunkumi ba.

Wato dai batun nan na yadda a farkon makon nan kungiyar EU ta amince da wasu tanade-tanade na kakabawa wasu sassa 84, da daidaikun mutane na wasu kasashe daban daban takunkumai, bisa zarfin wai suna taimakawa dakarun sojin Rasha da kayayyakin aiki, irin su sassan jirage marasa matuka, da sauran abubuwan harhada naurorin laturoni a rikicinta da Ukraine. Kuma 7 daga cikin wadancan sassa da takunkuman suka shafa sun fito ne daga kasar Sin.

  • Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu
  • Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

Ba dai wannan ne karon farko da EU ta dauki irin wannan mataki kan wasu sassa ciki har da daidaikun Sinawa ba, kuma a lokuta daban daban, irin wannan mataki kan hada da takunkumin hana tafiye-tafiye, da daskarar da kadarori, da hana damar samar da kudade, matakan da a baya EUn kan ce na shawo kan kalubalen fitar da hajoji ne.

Illar wannan mataki na EU, shi ne tarayyar Turai na aikewa da wani sako mai karfi ga bangaren Sin, cewa kungiyar na zargin Sin da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, duk da sanin cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne, kuma mataki ne da ka iya lahanta alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin EU da Sin.

Wani abun lura ma shi ne duk da cewa Amurka ta sha kakkaba wasu takunkumai kan kasar Sin, bisa zarginta da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, takunkuman da kuma suka fi tsauri sama da na EU, ba su sauya matsayar Sin na tsayawa bisa adalci, da kin goyon bayan wani bangare a rikicin bana, don haka ya kamata ita ma EU ta san cewa, Sin ba za ta yi watsi da sahihiyar manufarta ta kin goyon bayan rikici da ingiza sulhu ba. Kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta yi watsi da gudanar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da kasar Rasha kamar yadda aka saba tun tuni ba.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

A wannan gaba da alkaluma ke nuna yawan takunkuman da EU ta kakkabawa kasar Rasha ma sun kai zagaye na 15, ya dace EU ta lura cewa, ba za a iya warware rikicin Rasha da Ukraine ta hanyar kakkaba takunkumai ba, kuma Amurka ce ke da alhakin ingiza wutar rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin Rasha da Ukraine, da ma makamancinsa na Israila da Hamas a Gaza. Don haka, idan har neman wanda za a dorawa alhakin tashe-tashen hankula dake wakana a Turai da Gabas ta tsakiya ake yi, ya wajaba EU ta mayar da hankali ga Amurka, domin jin bahasi, muddin dai ana son tafiya bisa turbar gaskiya da adalci.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

Next Post

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

9 minutes ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

1 hour ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

2 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

3 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

5 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

23 hours ago
Next Post
PRP

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.