ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, ya ce hakan wani muhimmin tsari ne na amfani da damar da ke cikin ɓangaren kiwo da kuma inganta sarrafa kayayyakin da ake samarwa.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a lokacin da yake jawabi a Taron Shekara-shekara na Hukumar Gidajen Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) da aka gudanar a Abuja, mai taken “Samar da Abinci a Nijeriya: Ina Mafita?”

ADVERTISEMENT
  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina
  • Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Ya ce: “Ba a jima ba da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), ya ɗauki wani gagarumin mataki na kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi. Wannan tsari mai muhimmanci ya nuna yadda gwamnatin ta fahimci irin damar da ke cikin harkar kiwon dabbobi, wanda ake kira tushen da ba a yi amfani da shi ba.”

 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ministan ya jaddada cewa tabbatar da wadatar abinci yana da matuƙar muhimmanci ga tsaron ƙasa, zaman lafiya, da cin gashin kai.

 

Wannan ne ya sa Shugaba Tinubu ya sake fasalin sunan Ma’aikatar Noma da Raya Yankunan Karkara zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

 

Ya ce: “Nijeriya, wadda Allah ya albarkace ta da ƙasa mai yalwa, yanayi mai kyau, da matasa da ke cike da kuzari, tana da damar zama jagorar noma a duniya. Amma har yanzu muna fama da ƙalubale wajen samar da abinci mai arha kuma wadatacce.

 

“Wannan ƙalubale ne da ya sa Shugaban Ƙasa ya mai da hankali sosai ga wannan muhimmin ɓangare, wanda shi ne babbar hanyar samar da ayyukan yi a ƙasar nan.”

 

Idris ya bayyana cewa gwamnatin ta ɗauki matakai masu muhimmanci, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci kan samar da abinci, ƙaddamar da shirin samar da abinci mai ɗorewa, da kuma yaƙi da masu ɓoye kaya da masu fasa-ƙwauri, domin tabbatar da samun kayan abinci cikin sauƙi da arha.

 

“Babu abin da ba za a iya cimmawa ba wajen samar da abinci a Nijeriya, musamman idan muka haɗa kai; za mu iya canza ƙasar mu zuwa ƙasar da take da yalwar abinci, inda babu wani ɗan Nijeriya da zai kwanta da yunwa.

 

“Na tabbata cewa babban baƙo mai gabatar da jawabi da sauran ƙwararru za su yi cikakken bayani kan ƙalubalen da harkar noma ke fuskanta tare da bayar da hanyoyin magance su,” inji shi.

 

Ministan ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taka muhimmiyar rawa wajen inganta samar da abinci ta hanyar ilimantar da manoma kan dabarun zamani, canjin yanayi, da kuma tallafin da gwamnati ke bayarwa domin ƙara yawan amfanin gona.

 

Idris ya yaba wa FRCN bisa farfaɗo da wannan Taron Shekara-shekara ɗin, inda ya yaba da ƙudirin ta na bunƙasa cigaban ƙasa ta hanyar shirye-shirye da kuma tsare-tsare masu tasiri.

 

Taron ya samu halartar manyan baƙi kamar Ministan Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Muktar; Ƙaramin Ministan Noma da Tabbatar da Wadatar Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi; Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli; da Sarkin Wase a Jihar Filato, Alhaji Muhammadu Sambo Haruna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.