ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, ya ce hakan wani muhimmin tsari ne na amfani da damar da ke cikin ɓangaren kiwo da kuma inganta sarrafa kayayyakin da ake samarwa.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a lokacin da yake jawabi a Taron Shekara-shekara na Hukumar Gidajen Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) da aka gudanar a Abuja, mai taken “Samar da Abinci a Nijeriya: Ina Mafita?”

ADVERTISEMENT
  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina
  • Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Ya ce: “Ba a jima ba da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), ya ɗauki wani gagarumin mataki na kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi. Wannan tsari mai muhimmanci ya nuna yadda gwamnatin ta fahimci irin damar da ke cikin harkar kiwon dabbobi, wanda ake kira tushen da ba a yi amfani da shi ba.”

 

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Ministan ya jaddada cewa tabbatar da wadatar abinci yana da matuƙar muhimmanci ga tsaron ƙasa, zaman lafiya, da cin gashin kai.

 

Wannan ne ya sa Shugaba Tinubu ya sake fasalin sunan Ma’aikatar Noma da Raya Yankunan Karkara zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

 

Ya ce: “Nijeriya, wadda Allah ya albarkace ta da ƙasa mai yalwa, yanayi mai kyau, da matasa da ke cike da kuzari, tana da damar zama jagorar noma a duniya. Amma har yanzu muna fama da ƙalubale wajen samar da abinci mai arha kuma wadatacce.

 

“Wannan ƙalubale ne da ya sa Shugaban Ƙasa ya mai da hankali sosai ga wannan muhimmin ɓangare, wanda shi ne babbar hanyar samar da ayyukan yi a ƙasar nan.”

 

Idris ya bayyana cewa gwamnatin ta ɗauki matakai masu muhimmanci, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci kan samar da abinci, ƙaddamar da shirin samar da abinci mai ɗorewa, da kuma yaƙi da masu ɓoye kaya da masu fasa-ƙwauri, domin tabbatar da samun kayan abinci cikin sauƙi da arha.

 

“Babu abin da ba za a iya cimmawa ba wajen samar da abinci a Nijeriya, musamman idan muka haɗa kai; za mu iya canza ƙasar mu zuwa ƙasar da take da yalwar abinci, inda babu wani ɗan Nijeriya da zai kwanta da yunwa.

 

“Na tabbata cewa babban baƙo mai gabatar da jawabi da sauran ƙwararru za su yi cikakken bayani kan ƙalubalen da harkar noma ke fuskanta tare da bayar da hanyoyin magance su,” inji shi.

 

Ministan ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taka muhimmiyar rawa wajen inganta samar da abinci ta hanyar ilimantar da manoma kan dabarun zamani, canjin yanayi, da kuma tallafin da gwamnati ke bayarwa domin ƙara yawan amfanin gona.

 

Idris ya yaba wa FRCN bisa farfaɗo da wannan Taron Shekara-shekara ɗin, inda ya yaba da ƙudirin ta na bunƙasa cigaban ƙasa ta hanyar shirye-shirye da kuma tsare-tsare masu tasiri.

 

Taron ya samu halartar manyan baƙi kamar Ministan Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Muktar; Ƙaramin Ministan Noma da Tabbatar da Wadatar Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi; Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli; da Sarkin Wase a Jihar Filato, Alhaji Muhammadu Sambo Haruna.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.