• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kungiyoyin mata da matasa a jihar Bauchi sun yi gangami a ofishin Sanata Halliru Dauda Jika inda suke kiransa da ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NNPP mai alamar kwando da kayan marmari domin samun zarafin fitowa takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023 da ke tafe.

Wakilinmu ya labarto cewa Sanata Halliru Dauda Jika dai shine ke wakiltar mazabar Bauchi ta tsakiya a Majalisar Dattawa ya fito neman tikitin APC na kujerar gwamna amma Air Marshal Saddique Baba Abubakar ya kayar da shi a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a kwanakin baya.

  • Dubban Jama’a Sun Shiga Jam’iyyar NNPP A Neja

Da ya ke jawabi a wajen gangamin, Sadik Abdullahi Kobi, Shugaban kungiyar mata masu dogaro da kansu na jihar Bauchi, ya shaida cewar, babban burinsu shine Sanatan ya amince ya fito neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP domin cire musu kitse a wuta.

Mata

Ya ce: “Wannan dandanzon mata da matasa da ka gani sun fito ne domin yin kira ga Sanata Halliru Dauda Jika da ya fice daga jam’iyyar APC ya shiga jam’iyyar NNPP domin ya samu damar yin takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023.”

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

“Daman mun gargadi uwar jam’iyyar APC ta dauki tikitin neman takarar gwamna ta bai wa Sanata Jika saboda shi ne yake tare da mutane, shi ne yake mutunta mutane, shine ya san matsalolinsu, shine yake kawo cigaba ga kuma shine suke so, sabanin wanda aka zo aka kakaba mana da karfin tsiya. Don haka muke son ya bar jam’iyyar ya koma NNPP mu kuma muna tare da shi dari bisa dari.

“Don haka mu a matsayinmu na mata da matasa muna nuna wa Sanata Jika hanyar da ya dace na cewa ya zo ya bi abun da jama’a ke so. Abun da jama’a ke so kuma shine ya shiga NNPP ya mana takarar gwamna.”

Mata

Abdullahi Kobi ya bada tabbacin cewa muddin Jika ya amince ya fito neman takarar gwamna a NNPP tabbas jama’an jihar za su zabeshi domin sun amince da salon jagorancinsa da kyautata musu, “al’umma ke kawo mutum musamman mata. Ka ga kuwa al’ummar ne suka ce lallai ya zo ya musu takara. Don haka muna da kyakkyawar fatan shine zai yi nasara a babban zaben 2023.”

A bangarenta, Malama Saliha Abubakar ta bayyana cewar a shirye suke su shiga lungu da sako domin nema wa Sanata Jika kuri’u, tana mai cewa sun amince da cewa ya fi kowani dan takara dacewar da zai iya jagorantar jihar Bauchi yadda ya kamata.

“Mu iyaye mata mune mu kan irin halin da muke cikin a hali yanzu. Don haka muna rokon ya amsa kiran mu ya koma NNPP domin mu mara masa baya.”

Da ya ke amsar bukatun kungiyoyin a madadin Sanatan, Haruna Muhammad daya daga cikin hadiman Sanata Jika, ya gode wa kungiyoyin bisa nuna damuwa da soyayya ga Sanata Halliru Dauda Jika ya kuma ba su tabbacin cewa za su yi zama na musamman kan wannan bukatar tare da daukan matakin da ya dace domin cigaban jihar Bauchi.

Ya ce, tabbas Sanata Jika na yi ne don al’umma kuma zai sauraro bukatunsu tare da yin abun da dace. Ya ba su tabbacin cewa da izinin Allah Sanata Jika zai yi takarar gwamna a 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

Next Post

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Related

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da É—umi-É—uminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

11 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

3 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

3 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

4 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

4 days ago
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna
Siyasa

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

4 days ago
Next Post
Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.