• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin ‘Yan Daba: An Kashe Dan Shekara 15 Tare Da Cafke Mutum Biyar A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Rikicin ‘Yan Daba: An Kashe Dan Shekara 15 Tare Da Cafke Mutum Biyar A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kashe wani matashi dan shekara 15 mai suna Saidu Udu a wani rikici da ya barke a garin Minna na Jihar Neja a ranar Asabar.

Jami’an ‘yansanda sun cafke mutum biyar da ake zargi da yunkurin tserewa daga wurin.

  • Sin Ta Dauki Matakin Martani Kan Kamfanonin Makamai Na Amurka
  • Fiye Da Kaso 80 Na Kamfanonin Sin Sun Fadada Zuba Jari A Waje A 2024

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa jami’an sintiri nasu sun kai dauki amma tuni ‘yan dabar suka gudu.

Kakakin rundunar ‘yansandan, Wasiu Abiodun, a wani sakon WhatsApp da ya aike wa PUNCH Online, ya ce: “A ranar 21/12/2024 da misalin karfe 11:30 wasu ‘yan Daba daga yankin Gurgudu da ke Maitumbi da Kwari-Berger sun far ma juna, lamarin da ya kai ga mutuwar wani Saidu Udu, mai shekaru 15, daga Gurgudu. Tawagar ‘yansanda da ke sintiri daga sashin Maitumbi ta koma wurin da lamarin ya faru, amma ‘yan Dabar sun tsere. An kai wanda aka an tadi da wanda ya shafa zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

“A wani samame da aka kai a yankin, an kama wasu bata gari biyar. A yanzu haka ana gudanar da bincike, kuma ana ci gaba da kokarin kamo sauran ‘yan Dabar da suka tsere.”

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Rikicin, wanda rahotanni suka ce ya hada da ’yan iska fiye da 50, an ce ya samo asali ne daga rashin jituwa kan rabon kudaden Kirsimeti da ake zargin wani da ba a tantance ba ya ba su.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa ‘yan Dabar dauke da wukake, sun rikide zuwa tashin hankali, wanda ya kai ga caka wa Udu wuka a ciki.

Wani magidanci mai suna Malik Nurudeen ya bayyana yadda lamarin ya faru, ya ce, “’Ya’yan unguwar nan kullum suna zuwa suna yi mana barazana, amma a yau sun haura 50, da farko mun dauka kungiya daya ce, amma daga baya muka gano wasu kungiyoyi ne guda biyu. Daga gardamarsu, ya bayyana a fili cewa sun karbi kudin Kirsimeti daga wani amma sun kasa yarda da tsarin rabon kudin.

“Sun fara yi wa juna barazana da makamansu har sai da aka caka ma daya daga cikin su wuka, sannan kowa ya fara gudu,” in ji shi

.

Mazauna garin sun koka da yadda ake samun karuwar tashe-tashen hankula a Minna, tare da yin arangama akai-akai da ke barin wadanda abin ya shafa suka jikkata, ko kuma a kashe su.

Duk da kokarin da ‘yansanda suka yi na dakile ayyukan ‘yan iskan da aka fi sani da ‘Yan Daba (Area Boys), ‘yan ta’adda na ci gaba da addabar garin.

An bayar da rahoton cewa an kashe mutane da dama ko kuma raunatawa a yayin da ’yan ta’addan suka yi arangama, wadanda su kan kaucewa kamawa tare da ci gaba da munanan ayyukansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Shawulu Danmamman, ya bayar da tabbacin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Dauki Matakin Martani Kan Kamfanonin Makamai Na Amurka

Next Post

NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 days ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 days ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 week ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 week ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.