ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin ‘Yan Daba: An Kashe Dan Shekara 15 Tare Da Cafke Mutum Biyar A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 year ago
Yan daba

An kashe wani matashi dan shekara 15 mai suna Saidu Udu a wani rikici da ya barke a garin Minna na Jihar Neja a ranar Asabar.

Jami’an ‘yansanda sun cafke mutum biyar da ake zargi da yunkurin tserewa daga wurin.

  • Sin Ta Dauki Matakin Martani Kan Kamfanonin Makamai Na Amurka
  • Fiye Da Kaso 80 Na Kamfanonin Sin Sun Fadada Zuba Jari A Waje A 2024

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa jami’an sintiri nasu sun kai dauki amma tuni ‘yan dabar suka gudu.

ADVERTISEMENT

Kakakin rundunar ‘yansandan, Wasiu Abiodun, a wani sakon WhatsApp da ya aike wa PUNCH Online, ya ce: “A ranar 21/12/2024 da misalin karfe 11:30 wasu ‘yan Daba daga yankin Gurgudu da ke Maitumbi da Kwari-Berger sun far ma juna, lamarin da ya kai ga mutuwar wani Saidu Udu, mai shekaru 15, daga Gurgudu. Tawagar ‘yansanda da ke sintiri daga sashin Maitumbi ta koma wurin da lamarin ya faru, amma ‘yan Dabar sun tsere. An kai wanda aka an tadi da wanda ya shafa zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

“A wani samame da aka kai a yankin, an kama wasu bata gari biyar. A yanzu haka ana gudanar da bincike, kuma ana ci gaba da kokarin kamo sauran ‘yan Dabar da suka tsere.”

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Rikicin, wanda rahotanni suka ce ya hada da ’yan iska fiye da 50, an ce ya samo asali ne daga rashin jituwa kan rabon kudaden Kirsimeti da ake zargin wani da ba a tantance ba ya ba su.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa ‘yan Dabar dauke da wukake, sun rikide zuwa tashin hankali, wanda ya kai ga caka wa Udu wuka a ciki.

Wani magidanci mai suna Malik Nurudeen ya bayyana yadda lamarin ya faru, ya ce, “’Ya’yan unguwar nan kullum suna zuwa suna yi mana barazana, amma a yau sun haura 50, da farko mun dauka kungiya daya ce, amma daga baya muka gano wasu kungiyoyi ne guda biyu. Daga gardamarsu, ya bayyana a fili cewa sun karbi kudin Kirsimeti daga wani amma sun kasa yarda da tsarin rabon kudin.

“Sun fara yi wa juna barazana da makamansu har sai da aka caka ma daya daga cikin su wuka, sannan kowa ya fara gudu,” in ji shi

.

Mazauna garin sun koka da yadda ake samun karuwar tashe-tashen hankula a Minna, tare da yin arangama akai-akai da ke barin wadanda abin ya shafa suka jikkata, ko kuma a kashe su.

Duk da kokarin da ‘yansanda suka yi na dakile ayyukan ‘yan iskan da aka fi sani da ‘Yan Daba (Area Boys), ‘yan ta’adda na ci gaba da addabar garin.

An bayar da rahoton cewa an kashe mutane da dama ko kuma raunatawa a yayin da ’yan ta’addan suka yi arangama, wadanda su kan kaucewa kamawa tare da ci gaba da munanan ayyukansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Shawulu Danmamman, ya bayar da tabbacin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan.

Yan daba
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Yan daba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.