• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Mutane da dama ne suka taya Dr. Maryam Mansur Yola murnar zama Farfesa kan magungunan gargajiya da al'adu a shafukan sada zumunta.

by Muhammad and Naziru Adam Ibrahim
8 months ago
in Al'adu, Adabi, Ilimi
0
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Gudanarwar Jami’ar Bayero da ke Kano, ta amince da É—aga darajar Dr. Maryam Mansur Yola, ta Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, da ke Jami’ar zuwa matsayin Farfesar Magungunan Gargajiya da Al’adu, kamar yadda wata sanarwa da Jami’ar ta fitar a ranar Juma’a 27 ga Disamba, 2024 ta bayyana.

Farfesa Maryam Yola, ‘yar asalin Æ™aramar hukumar Kano Municipal, ita ce mace ta farko a tarihi da ta zama farfesa kan magungunan gargajiya da al’adun Hausa, kuma malama ce da ke koyar da kwasa-kwasan Al’adun Bahaushe da ta koyar da É—umbin É—alibai a matakan ilimin daban-daban a ciki da wajen Nijeriya.

  • ÆŠaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da ÆŠakin Karatu Na M.A.Z Sani
  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Farfesa Yola, mace ce da ta yi fice kan bincike a fannin magungunan gargajiya tun daga digirinta na farko, inda ta yi akan darussan Hausa a shekarar 1990, ta yi digirinta na biyu kan al’adun Bahaushe a shekarar 1997. Farfesa Yola ta kuma kammala karatunta na digiri na uku a shekara ta 2017, duka a Jami’ar Bayero. Kazalika, Farfesar ta yi babbar difiloma kan harkokin koyar da ilmi (PDE) a Kwalejin Shari’a ta Malam Aminu Kano (Legal) da ke Kano, inda ta kammala a shekarar 2015, ta kuma samu Æ™arin wasu takardun shaidar ilimi a wasu kwasa-kwasai da dama.

Baya ga takardu da maÆ™alu masu tarin yawa da ta gabatar kan magungunan gargajiya a jami’o’i da makarantu da wuraren tarukan ilimi daban-daban a ciki da wajen Nijeriya, ta duba aikin É—alibai masu tarin yawa a matakin digiri na É—aya da na biyu da na uku a Jami’ar Bayero da wasu Jami’o’i a Nijeriya.

Farfesa Yola, ta kuma riÆ™e muÆ™amai da dama a matakin gwamnatin tarayya da jiha da wasu kungiyoyin siyasa da jami’a da Æ™ungiyoyin ci gaban al’umma.

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A 8-8-2025

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Farfesa Mansur Yola, mamba ce a Ƙungiyar malaman Jami’o’i ta Æ™asa (ASUU), kazalika mamba ce a Ƙungiyar Mata ta (ASFECOM), da kuma hukumar da ke bayar da shaidar malanta ta Nijeriya (TRCN).

A zamanin mulkin Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ta riƙe Shugabar Hukumar Ilimin bai-ɗaya ta Jihar Kano daga 2008 zuwa 2011, da sauran muƙaman gwamnati da siyasa da dama a matakai daban-daban.

Ana sa ran É—aga darajar Fafesar zuwa wannan mataki zai Æ™ara mata himma da Æ™warin gwuiwar ci gaba da bayar da gudunmowa wajen inganta harkokin magungunan gargajiya a Nijeriya, ta hanyar amfani da É—imbin ilimi da Æ™warewarta a fannin, tare da bunÆ™asa al’adun Hausa, da cike giÉ“in da ake da shi a É“angarorin magungunan gargajiya da al’adun Hausa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKFarfesa Maryam Mansur YolaHausaJami'ar Bayero KanoSashen Koyar da Harsunan NijeriyaYola
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Cire Tallafin Mai Da Gyaran Dokar Haraji, Bankin Duniya Ya Danƙa Wa Nijeriya Bashi

Next Post

Yankin Xinjiang Na Kasar Sin Ya Kammala Aikin Shimfida Rami Mafi Tsawo A Duniya

Related

GORON JUMA’A 8-8-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 8-8-2025

5 days ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

1 week ago
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

3 weeks ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

3 weeks ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

4 weeks ago
Next Post
Yankin Xinjiang Na Kasar Sin Ya Kammala Aikin Shimfida Rami Mafi Tsawo A Duniya

Yankin Xinjiang Na Kasar Sin Ya Kammala Aikin Shimfida Rami Mafi Tsawo A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.