• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa suna da wani karin magana mai ban sha’awa da ke kara shaja’antar da mazumunta a kan kara dankon zumunci a tsakaninsu, shi ne “zumunta a kafa take”.

Yayin da sabuwar shekarar 2025 ta fara lulawa, kasar Sin ta fara sauke hakkinta na yaukaka zumunci a tsakaninta da nahiyar Afirka ta hanyar fara ziyarar ministan harkokinta na waje, Wang Yi a wasu kasashe hudu na nahiyar da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da kuma Nijeriya.

  • An Kashe ’Yan Ta’adda 34 Da Sojoji 6 A Harin Borno – Shalkwatar Tsaro
  • Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Ziyarar ta kasance wani bangare na fara shirye-shiryen aiwatar da tsare-tsare 10 da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi wa nahiyar Afirka albishir da su a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a watan Satumban bara.

Sin da Afirka sun yanke shawarar daga matsayin dangantakarsu zuwa kololuwa da za ta karade dukkan fannoni na ci gaba a sabon zamani. Wannan zumunci yana ci gaba da haifar da da mai ido saboda yadda ake gudanar da harkoki a karkashinsa bisa gaskiya da amana ba tare da kumbiya-kumbiya ba. Inda hakan ya taimaka ga raya ababen more rayuwa a Afirka.

Cikin shekaru 25 da suka gabata kacal, kamfanonin kasar Sin da suka zuba jari a nahiyar Afirka sun taimaka wa kasashen yankin da ginawa ko kara inganta sufurin jirgin kasa da ya kunshi layukan dogo fiye da kilomita 10,000, da manyan tituna da tsawonsu ya kai kusan kilomita 100,000, da gina manyan gadoji kimanin 1,000, baya ga tasoshin jiragen ruwa ciki har da masu zurfin ruwa da adadinsu ya kai 100, kana da habaka samar da wutar lantarki ta hanyar gina tasoshin janyowa da layukan rarrabawa da a kalla za su kai tsawon kilomita 66,000.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Kasar Sin ta kuma himmatu wajen tallafa wa Afirka wajen gina masana’antu da za su rika sarrafa ko san’anta kayayyaki a cikin gida domin taimaka wa habakar tattalin arzikin yankin. Haka nan a bangaren ci gaban kimiyya da fasaha da aiki da sabbin makamashi marasa gurbata muhalli, kana bangaren aikin gona ma ba a bar shi a baya ba.

A tsakanin shekarun da ba su wuce 10 ba, kasar Sin ta gina cibiyoyin inganta fasahar aikin gona guda 24 a sassan Afirka tare da habaka fasahohin aikin gona daban-daban fiye da 300 wanda hakan ya taimaka gaya ga samun girbi mai albarka da a kalla kashi 30 zuwa 60 cikin dari inda manoma kimanin miliyan daya suka ci gajiyar abin.

Irin wannan zumunci ake so ya dawwama ana sadar da shi saboda kamar yadda Hausawa kan ce “na ji dadi shi ne batu, ba na saba ba!”(Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

Next Post

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

1 hour ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

19 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

20 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

22 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

23 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.