• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar na maraba da sabuwar shekarar nan ta 2025, ya jaddada aniyar kasarsa ta ci gaba da aiki tare da sauran kasashen duniya, don kara inganta koyi da juna tsakanin mabanbantan aladu da wayewar kai. Wadannan kalamai na shugaba Xi, shaida ce dake kara fito da shirin kasar Sin fili, a fannin amfani da kwarewa, da hangen nesa wajen ingiza kyakkyawan yanayin zaman tare tsakanin wayewar kai daban daban, da ma kwazon kasar na sauke nauyin dake wuyanta, na yayata ci gaban wayewar kan daukacin bil adama.

Ko shakka babu duniyar yau tana cike da sabbin yanayi na tangal-tangal, da sauye-sauye, yayin da karin kalubale ke bullowar duniya. Kuma magance manyan kalubalen dake addabar dan adam na bukatar wanzar da zaman lafiya, da zaman jiyuwa tsakanin mabanbantan wayewar kai.

  • Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka

A gani na, yayin da wasu sassan kasa da kasa ke aiwatar da matakan ware kai, da baiwa kasuwa kariya, da nuna fifiko, kasar Sin a nata bangare ta rungumi matakai masu kyau na sada zumunta da sauran sassa, ta hanyar musaya, da koyi da juna, matakan da za su baiwa sassan kasa da kasa damar amfana daga wayewar kan kasar Sin, wanda ya samo asali daga tarihinta na sama da shekaru 5,000.

Sanin kowa ne cewa cin gajiyar wayewar kai, da bunkasa rayuwar dan adam ba za su samu ba, muddin ba a cimma matsaya, da budewa juna kofa, da yin tafiya tare, da musaya, da koyi da juna tsakanin mabambantan wayewar kai ba. Kara tattaunawa zai rage fito na fito, yayin da yin tafiya tare zai rage rashin fahimtar juna. Hakan ne ma ya sa a watan Yunin shekarar 2024 da ta gabata, babban taron MDD karo na 78, da babban rinjaye ya amince da kudurin da kasar Sin ta gabatar, na kafa ranar kasa da kasa ta tattaunawa tsakanin mabanbantan wayewar kai. Wani mataki da a gani na ya zama misali, na yadda kasar ta Sin ke gabatarwa duniya dabarun warware wasu manyan matsaloli, musamman a wannan gaba da nufin kawar da kyamar juna, da ingiza fahimtar juna, da kyautata amincewa juna tsakanin sassan kasa da kasa.

A daya bangaren kuma, cimma burin zamanantarwa muhimmin batu ne mai nasaba da fatan bunkasa wayewar kan dan adam. Zamanantarwa ba aiki ne da ya shafi wasu tsirarun kasashe kalilan ba, kana ba zai yiwu ya zamo salo daya tak da za a kwafa daga wani yanki a kai wani yanki ba. A tafiyar zamanantarwa, kasar Sin ta yi imani da yin tafiya, da aiki tare da sauran kasashe, ta yadda za su hada karfi da karfe wajen yin musayar kwarewa, har a kai ga gina kasashe daban daban, da gina alummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya, wadda daukacin bil adama zai yi alfahari da ita.(Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang

Next Post

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Related

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

2 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

2 hours ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

18 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

20 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

21 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

23 hours ago
Next Post
Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.