ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

A cikin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar na maraba da sabuwar shekarar nan ta 2025, ya jaddada aniyar kasarsa ta ci gaba da aiki tare da sauran kasashen duniya, don kara inganta koyi da juna tsakanin mabanbantan aladu da wayewar kai. Wadannan kalamai na shugaba Xi, shaida ce dake kara fito da shirin kasar Sin fili, a fannin amfani da kwarewa, da hangen nesa wajen ingiza kyakkyawan yanayin zaman tare tsakanin wayewar kai daban daban, da ma kwazon kasar na sauke nauyin dake wuyanta, na yayata ci gaban wayewar kan daukacin bil adama.

Ko shakka babu duniyar yau tana cike da sabbin yanayi na tangal-tangal, da sauye-sauye, yayin da karin kalubale ke bullowar duniya. Kuma magance manyan kalubalen dake addabar dan adam na bukatar wanzar da zaman lafiya, da zaman jiyuwa tsakanin mabanbantan wayewar kai.

  • Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka

A gani na, yayin da wasu sassan kasa da kasa ke aiwatar da matakan ware kai, da baiwa kasuwa kariya, da nuna fifiko, kasar Sin a nata bangare ta rungumi matakai masu kyau na sada zumunta da sauran sassa, ta hanyar musaya, da koyi da juna, matakan da za su baiwa sassan kasa da kasa damar amfana daga wayewar kan kasar Sin, wanda ya samo asali daga tarihinta na sama da shekaru 5,000.

ADVERTISEMENT

Sanin kowa ne cewa cin gajiyar wayewar kai, da bunkasa rayuwar dan adam ba za su samu ba, muddin ba a cimma matsaya, da budewa juna kofa, da yin tafiya tare, da musaya, da koyi da juna tsakanin mabambantan wayewar kai ba. Kara tattaunawa zai rage fito na fito, yayin da yin tafiya tare zai rage rashin fahimtar juna. Hakan ne ma ya sa a watan Yunin shekarar 2024 da ta gabata, babban taron MDD karo na 78, da babban rinjaye ya amince da kudurin da kasar Sin ta gabatar, na kafa ranar kasa da kasa ta tattaunawa tsakanin mabanbantan wayewar kai. Wani mataki da a gani na ya zama misali, na yadda kasar ta Sin ke gabatarwa duniya dabarun warware wasu manyan matsaloli, musamman a wannan gaba da nufin kawar da kyamar juna, da ingiza fahimtar juna, da kyautata amincewa juna tsakanin sassan kasa da kasa.

A daya bangaren kuma, cimma burin zamanantarwa muhimmin batu ne mai nasaba da fatan bunkasa wayewar kan dan adam. Zamanantarwa ba aiki ne da ya shafi wasu tsirarun kasashe kalilan ba, kana ba zai yiwu ya zamo salo daya tak da za a kwafa daga wani yanki a kai wani yanki ba. A tafiyar zamanantarwa, kasar Sin ta yi imani da yin tafiya, da aiki tare da sauran kasashe, ta yadda za su hada karfi da karfe wajen yin musayar kwarewa, har a kai ga gina kasashe daban daban, da gina alummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya, wadda daukacin bil adama zai yi alfahari da ita.(Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Sin

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.