ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Adc

Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Sanata David Mark, ya bayyana jam’iyyar a matsayin wata hanya da za a bi don cimma haɗin kan Arewa, da cigaba da kawo ci gaban yankin. Ya bayyana haka ne a jawabin buɗe taro na uku na babbar ganawar ƙungiyar tuntuɓa a siyasa (NPCG) ta Arewa, a Abuja.

Taron wanda ya gudana bayan bayyana ADC a matsayin sabon dandalin siyasa ga wasu fitattun ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027, ya nemi hanyoyin da za a bi wajen haɗa kan al’ummar Arewa. A taro na baya, ƙungiyar NPCG ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ta bukaci a gaggauta bayyana wata sabuwar jam’iyya domin kare muradun yankin.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

A cewar Sanata Mark, Arewa na cikin wani hali mai sosa rai, yana mai jaddada cewa ‘yan Arewa su ne za su iya magance matsalolin da ke damun su. Ya buƙaci a guji maganganu masu tayar da fitina da siyasar rarrabuwa, tare da mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar ilimi, da kiwon lafiya da ababen more rayuwa.

ADVERTISEMENT

Sanata Mark ya bayyana cewa duk da albarkatun ƙasa, arziƙin noma, da yawan al’adu, Arewa na fama da matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, talauci, rikice-rikicen ƙabilanci da na addini, da kuma gazawar ci gaban tattalin arziki da siyasa. Ya bayyana yadda rashin tsaro ke hana masu zuba jari shiga yankin, wanda ke ƙara ƙarfafa fatara da laifuka.

Ya koka kan yadda ake amfani da ƙabilanci da addini wajen haifar da rikice-rikice don biyan buƙatun wasu. Ya buƙaci al’umma su koma ga zaman lafiya da juna da suka yi fice da shi a baya, inda kalmar “Ɗan Arewa” ke bayyana duƙulalliyar halayyarsu. Mark ya jaddada cewa ADC za ta kawo bambanci, domin a wajensu siyasa ibada ce, ba hanya ta yaudara ba. Ya ƙara da cewa dole ne Arewa ta farka daga wannan yanayi, domin a da yankin ne mafi aminci a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

Adc
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Mutane 31 A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kano Ta Kulle Shagon Maganin Gargajiya Saboda Batsa
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Gurfanar Da Jami’in NDLEA Bisa Zargin Yi Wa Yarinya Fyaɗe

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Adc

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Adc

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.