ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Adc

Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Sanata David Mark, ya bayyana jam’iyyar a matsayin wata hanya da za a bi don cimma haɗin kan Arewa, da cigaba da kawo ci gaban yankin. Ya bayyana haka ne a jawabin buɗe taro na uku na babbar ganawar ƙungiyar tuntuɓa a siyasa (NPCG) ta Arewa, a Abuja.

Taron wanda ya gudana bayan bayyana ADC a matsayin sabon dandalin siyasa ga wasu fitattun ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027, ya nemi hanyoyin da za a bi wajen haɗa kan al’ummar Arewa. A taro na baya, ƙungiyar NPCG ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ta bukaci a gaggauta bayyana wata sabuwar jam’iyya domin kare muradun yankin.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

A cewar Sanata Mark, Arewa na cikin wani hali mai sosa rai, yana mai jaddada cewa ‘yan Arewa su ne za su iya magance matsalolin da ke damun su. Ya buƙaci a guji maganganu masu tayar da fitina da siyasar rarrabuwa, tare da mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar ilimi, da kiwon lafiya da ababen more rayuwa.

ADVERTISEMENT

Sanata Mark ya bayyana cewa duk da albarkatun ƙasa, arziƙin noma, da yawan al’adu, Arewa na fama da matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, talauci, rikice-rikicen ƙabilanci da na addini, da kuma gazawar ci gaban tattalin arziki da siyasa. Ya bayyana yadda rashin tsaro ke hana masu zuba jari shiga yankin, wanda ke ƙara ƙarfafa fatara da laifuka.

Ya koka kan yadda ake amfani da ƙabilanci da addini wajen haifar da rikice-rikice don biyan buƙatun wasu. Ya buƙaci al’umma su koma ga zaman lafiya da juna da suka yi fice da shi a baya, inda kalmar “Ɗan Arewa” ke bayyana duƙulalliyar halayyarsu. Mark ya jaddada cewa ADC za ta kawo bambanci, domin a wajensu siyasa ibada ce, ba hanya ta yaudara ba. Ya ƙara da cewa dole ne Arewa ta farka daga wannan yanayi, domin a da yankin ne mafi aminci a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

Adc
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Babu Dalilin Da Zai Sa Nijeriya Yin Talauci – Obasanjo
  • Abubakar Sulaiman
    Air Peace Da United Nigeria, Jirage 2 Masu Latti Sosai Watan Agusta — NCAA
  • Abubakar Sulaiman
    Abubuwa 5 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Abubakar Sulaiman
    Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

MASU ALAKA

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II
Manyan Labarai

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

September 17, 2026
Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu
Labarai

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

September 17, 2026
2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa
Manyan Labarai

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
Next Post
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing

September 17, 2026
Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

September 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

September 17, 2026
Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

September 17, 2026
Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

September 17, 2026
 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

September 17, 2026
2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026
Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.